< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
A psalm of Asaph. Surely God is good to Israel, to those with a pure heart.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
But as for me, my feet almost slipped; my feet almost slipped out from under me
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
because I was envious of the arrogant when I saw the prosperity of the wicked.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
For they have no pain until their death, but they are strong and well fed.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
They are free from the burdens of other men; they are not afflicted like other men.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Pride adorns them like a necklace around their neck; violence clothes them like a robe.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Out of such blindness comes sin; evil thoughts pass through their hearts.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
They mock and speak wickedly; in their arrogance they threaten oppression.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
They set their mouth against the heavens, and their tongues march through the earth.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Therefore his people turn to them and abundant waters are drained out.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
They say, “How does God know? Is there knowledge with the Most High?”
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Take notice: these people are wicked; they are always carefree, becoming richer and richer.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Surely it is in vain that I have guarded my heart and washed my hands in innocence.
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
For all the day long I have been afflicted and disciplined every morning.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
If I had said, “I will say these things,” then I would have betrayed this generation of your children.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
Though I tried to understand these things, it was too difficult for me.
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
Then I went into God's sanctuary and came to understand their fate.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Surely you put them in slippery places; you bring them down to ruin.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
How they become a wilderness in a moment! They come to an end and are finished in awful terrors.
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
They are like a dream after one wakes up; Lord, when you arise, you will think nothing of those dreams.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
For my heart was grieved, and I was deeply wounded.
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
I was ignorant and lacked insight; I was like a senseless animal before you.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Yet I am always with you; you hold my right hand.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
You will guide me with your advice and afterward receive me to glory.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Whom have I in heaven but you? There is no one on earth that I desire but you.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
My flesh and my heart grow weak, but God is the strength of my heart forever.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
Those who are far from you will perish; you will destroy all those who are unfaithful to you.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
But as for me, all I need to do is to approach God. I have made the Lord Yahweh my refuge. I will declare all your deeds.

< Zabura 73 >