< Zabura 60 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
For the Chief Musician. To the tune of “The Lily of the Covenant.” A teaching poem by David, when he fought with Aram Naharaim and with Aram Zobah, and Joab returned, and killed twelve thousand of Edom in the Valley of Salt. God, you have rejected us. You have broken us down. You have been angry. Restore us, again.
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
You have made the land tremble. You have torn it. Mend its fractures, for it quakes.
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
You have shown your people hard things. You have made us drink the wine that makes us stagger.
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
You have given a banner to those who fear you, that it may be displayed because of the truth. (Selah)
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
So that your beloved may be delivered, save with your right hand, and answer us.
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God has spoken from his sanctuary: “I will triumph. I will divide Shechem, and measure out the valley of Succoth.
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
Gilead is mine, and Manasseh is mine. Ephraim also is the defense of my head. Judah is my scepter.
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
Moab is my wash basin. I will throw my sandal on Edom. I shout in triumph over Philistia.”
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
Who will bring me into the strong city? Who has led me to Edom?
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Haven’t you, God, rejected us? You don’t go out with our armies, God.
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give us help against the adversary, for the help of man is vain.
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
Through God we will do valiantly, for it is he who will tread down our adversaries.

< Zabura 60 >