< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
A Psalm by Asaph. The Mighty One, God, Yahweh, speaks, and calls the earth from sunrise to sunset.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Out of Zion, the perfection of beauty, God shines out.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Our God comes, and does not keep silent. A fire devours before him. It is very stormy around him.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
He calls to the heavens above, to the earth, that he may judge his people:
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
“Gather my saints together to me, those who have made a covenant with me by sacrifice.”
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
The heavens shall declare his righteousness, for God himself is judge. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
“Hear, my people, and I will speak. Israel, I will testify against you. I am God, your God.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
I don’t rebuke you for your sacrifices. Your burnt offerings are continually before me.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I have no need for a bull from your stall, nor male goats from your pens.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
For every animal of the forest is mine, and the livestock on a thousand hills.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I know all the birds of the mountains. The wild animals of the field are mine.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I were hungry, I would not tell you, for the world is mine, and all that is in it.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Will I eat the meat of bulls, or drink the blood of goats?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Offer to God the sacrifice of thanksgiving. Pay your vows to the Most High.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Call on me in the day of trouble. I will deliver you, and you will honor me.”
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
But to the wicked God says, “What right do you have to declare my statutes, that you have taken my covenant on your lips,
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
since you hate instruction, and throw my words behind you?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
When you saw a thief, you consented with him, and have participated with adulterers.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
“You give your mouth to evil. Your tongue frames deceit.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
You sit and speak against your brother. You slander your own mother’s son.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
You have done these things, and I kept silent. You thought that I was just like you. I will rebuke you, and accuse you in front of your eyes.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
“Now consider this, you who forget God, lest I tear you into pieces, and there be no one to deliver.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Whoever offers the sacrifice of thanksgiving glorifies me, and prepares his way so that I will show God’s salvation to him.”

< Zabura 50 >