< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
For the Chief Musician. A Psalm by David. Blessed is he who considers the poor. Yahweh will deliver him in the day of evil.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
Yahweh will preserve him, and keep him alive. He shall be blessed on the earth, and he will not surrender him to the will of his enemies.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
Yahweh will sustain him on his sickbed, and restore him from his bed of illness.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
I said, “Yahweh, have mercy on me! Heal me, for I have sinned against you.”
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
My enemies speak evil against me: “When will he die, and his name perish?”
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
If he comes to see me, he speaks falsehood. His heart gathers iniquity to itself. When he goes abroad, he tells it.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
All who hate me whisper together against me. They imagine the worst for me.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
“An evil disease”, they say, “has afflicted him. Now that he lies he shall rise up no more.”
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Yes, my own familiar friend, in whom I trusted, who ate bread with me, has lifted up his heel against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But you, Yahweh, have mercy on me, and raise me up, that I may repay them.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this I know that you delight in me, because my enemy doesn’t triumph over me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
As for me, you uphold me in my integrity, and set me in your presence forever.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Blessed be Yahweh, the God of Israel, from everlasting and to everlasting! Amen and amen.

< Zabura 41 >