< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
A Psalm by David, for a memorial. Yahweh, don’t rebuke me in your wrath, neither chasten me in your hot displeasure.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
For your arrows have pierced me, your hand presses hard on me.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
There is no soundness in my flesh because of your indignation, neither is there any health in my bones because of my sin.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
For my iniquities have gone over my head. As a heavy burden, they are too heavy for me.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
My wounds are loathsome and corrupt because of my foolishness.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
I am in pain and bowed down greatly. I go mourning all day long.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
For my waist is filled with burning. There is no soundness in my flesh.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
I am faint and severely bruised. I have groaned by reason of the anguish of my heart.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Lord, all my desire is before you. My groaning is not hidden from you.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
My heart throbs. My strength fails me. As for the light of my eyes, it has also left me.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
My lovers and my friends stand aloof from my plague. My kinsmen stand far away.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
They also who seek after my life lay snares. Those who seek my hurt speak mischievous things, and meditate deceits all day long.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
But I, as a deaf man, don’t hear. I am as a mute man who doesn’t open his mouth.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Yes, I am as a man who doesn’t hear, in whose mouth are no reproofs.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
For I hope in you, Yahweh. You will answer, Lord my God.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
For I said, “Don’t let them gloat over me, or exalt themselves over me when my foot slips.”
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
For I am ready to fall. My pain is continually before me.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
For I will declare my iniquity. I will be sorry for my sin.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
But my enemies are vigorous and many. Those who hate me without reason are numerous.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
They who render evil for good are also adversaries to me, because I follow what is good.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Don’t forsake me, Yahweh. My God, don’t be far from me.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Hurry to help me, Lord, my salvation.

< Zabura 38 >