< Zabura 36 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
For the Chief Musician. By David, the servant of Yahweh. A revelation is within my heart about the disobedience of the wicked: There is no fear of God before his eyes.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
For he flatters himself in his own eyes, too much to detect and hate his sin.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
The words of his mouth are iniquity and deceit. He has ceased to be wise and to do good.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
He plots iniquity on his bed. He sets himself in a way that is not good. He doesn’t abhor evil.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Your loving kindness, Yahweh, is in the heavens. Your faithfulness reaches to the skies.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Your righteousness is like the mountains of God. Your judgments are like a great deep. Yahweh, you preserve man and animal.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
How precious is your loving kindness, God! The children of men take refuge under the shadow of your wings.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
They shall be abundantly satisfied with the abundance of your house. You will make them drink of the river of your pleasures.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
For with you is the spring of life. In your light we will see light.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Oh continue your loving kindness to those who know you, your righteousness to the upright in heart.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Don’t let the foot of pride come against me. Don’t let the hand of the wicked drive me away.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
There the workers of iniquity are fallen. They are thrust down, and shall not be able to rise.

< Zabura 36 >