< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
By David; when he pretended to be insane before Abimelech, who drove him away, and he departed. I will bless Yahweh at all times. His praise will always be in my mouth.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
My soul shall boast in Yahweh. The humble shall hear of it and be glad.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Oh magnify Yahweh with me. Let’s exalt his name together.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
I sought Yahweh, and he answered me, and delivered me from all my fears.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
They looked to him, and were radiant. Their faces shall never be covered with shame.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
This poor man cried, and Yahweh heard him, and saved him out of all his troubles.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
Yahweh’s angel encamps around those who fear him, and delivers them.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Oh taste and see that Yahweh is good. Blessed is the man who takes refuge in him.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Oh fear Yahweh, you his saints, for there is no lack with those who fear him.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
The young lions do lack, and suffer hunger, but those who seek Yahweh shall not lack any good thing.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Come, you children, listen to me. I will teach you the fear of Yahweh.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Who is someone who desires life, and loves many days, that he may see good?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Keep your tongue from evil, and your lips from speaking lies.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Depart from evil, and do good. Seek peace, and pursue it.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Yahweh’s eyes are toward the righteous. His ears listen to their cry.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
Yahweh’s face is against those who do evil, to cut off their memory from the earth.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
The righteous cry, and Yahweh hears, and delivers them out of all their troubles.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Yahweh is near to those who have a broken heart, and saves those who have a crushed spirit.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Many are the afflictions of the righteous, but Yahweh delivers him out of them all.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
He protects all of his bones. Not one of them is broken.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Evil shall kill the wicked. Those who hate the righteous shall be condemned.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Yahweh redeems the soul of his servants. None of those who take refuge in him shall be condemned.

< Zabura 34 >