< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
A Psalm by David, when he fled from Absalom his son. Yahweh, how my adversaries have increased! Many are those who rise up against me.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Many there are who say of my soul, “There is no help for him in God.” (Selah)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
But you, Yahweh, are a shield around me, my glory, and the one who lifts up my head.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
I cry to Yahweh with my voice, and he answers me out of his holy hill. (Selah)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
I laid myself down and slept. I awakened, for Yahweh sustains me.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
I will not be afraid of tens of thousands of people who have set themselves against me on every side.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Arise, Yahweh! Save me, my God! For you have struck all of my enemies on the cheek bone. You have broken the teeth of the wicked.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Salvation belongs to Yahweh. May your blessing be on your people. (Selah)

< Zabura 3 >