< Zabura 28 >

1 Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
By David. To you, Yahweh, I call. My rock, don’t be deaf to me, lest, if you are silent to me, I would become like those who go down into the pit.
2 Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
Hear the voice of my petitions, when I cry to you, when I lift up my hands toward your Most Holy Place.
3 Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
Don’t draw me away with the wicked, with the workers of iniquity who speak peace with their neighbors, but mischief is in their hearts.
4 Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
Give them according to their work, and according to the wickedness of their doings. Give them according to the operation of their hands. Bring back on them what they deserve.
5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
Because they don’t respect the works of Yahweh, nor the operation of his hands, he will break them down and not build them up.
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
Blessed be Yahweh, because he has heard the voice of my petitions.
7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
Yahweh is my strength and my shield. My heart has trusted in him, and I am helped. Therefore my heart greatly rejoices. With my song I will thank him.
8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
Yahweh is their strength. He is a stronghold of salvation to his anointed.
9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Save your people, and bless your inheritance. Be their shepherd also, and bear them up forever.

< Zabura 28 >