< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Why do the nations rage, and the peoples plot a vain thing?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
The kings of the earth take a stand, and the rulers take counsel together, against Yahweh, and against his Anointed, saying,
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
“Let’s break their bonds apart, and cast their cords from us.”
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
He who sits in the heavens will laugh. The Lord will have them in derision.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Then he will speak to them in his anger, and terrify them in his wrath:
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
“Yet I have set my King on my holy hill of Zion.”
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
I will tell of the decree: Yahweh said to me, “You are my son. Today I have become your father.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Ask of me, and I will give the nations for your inheritance, the uttermost parts of the earth for your possession.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
You shall break them with a rod of iron. You shall dash them in pieces like a potter’s vessel.”
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Now therefore be wise, you kings. Be instructed, you judges of the earth.
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Serve Yahweh with fear, and rejoice with trembling.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Give sincere homage to the Son, lest he be angry, and you perish on the way, for his wrath will soon be kindled. Blessed are all those who take refuge in him.

< Zabura 2 >