< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
A Psalm by David. Yahweh, who shall dwell in your sanctuary? Who shall live on your holy hill?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
He who walks blamelessly and does what is right, and speaks truth in his heart;
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
he who doesn’t slander with his tongue, nor does evil to his friend, nor casts slurs against his fellow man;
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
in whose eyes a vile man is despised, but who honors those who fear Yahweh; he who keeps an oath even when it hurts, and doesn’t change;
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
he who doesn’t lend out his money for usury, nor take a bribe against the innocent. He who does these things shall never be shaken.

< Zabura 15 >