< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Praise Yah, for it is good to sing praises to our God; for it is pleasant and fitting to praise him.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Yahweh builds up Jerusalem. He gathers together the outcasts of Israel.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
He heals the broken in heart, and binds up their wounds.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
He counts the number of the stars. He calls them all by their names.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Great is our Lord, and mighty in power. His understanding is infinite.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Yahweh upholds the humble. He brings the wicked down to the ground.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Sing to Yahweh with thanksgiving. Sing praises on the harp to our God,
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
who covers the sky with clouds, who prepares rain for the earth, who makes grass grow on the mountains.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
He provides food for the livestock, and for the young ravens when they call.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
He doesn’t delight in the strength of the horse. He takes no pleasure in the legs of a man.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Yahweh takes pleasure in those who fear him, in those who hope in his loving kindness.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Praise Yahweh, Jerusalem! Praise your God, Zion!
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
For he has strengthened the bars of your gates. He has blessed your children within you.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
He makes peace in your borders. He fills you with the finest of the wheat.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
He sends out his commandment to the earth. His word runs very swiftly.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
He gives snow like wool, and scatters frost like ashes.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
He hurls down his hail like pebbles. Who can stand before his cold?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
He sends out his word, and melts them. He causes his wind to blow, and the waters flow.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
He shows his word to Jacob, his statutes and his ordinances to Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
He has not done this for just any nation. They don’t know his ordinances. Praise Yah!

< Zabura 147 >