< Zabura 142 >

1 Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
A contemplation by David, when he was in the cave. A Prayer. I cry with my voice to Yahweh. With my voice, I ask Yahweh for mercy.
2 Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
I pour out my complaint before him. I tell him my troubles.
3 Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
When my spirit was overwhelmed within me, you knew my route. On the path in which I walk, they have hidden a snare for me.
4 Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
Look on my right, and see; for there is no one who is concerned for me. Refuge has fled from me. No one cares for my soul.
5 Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
I cried to you, Yahweh. I said, “You are my refuge, my portion in the land of the living.”
6 Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
Listen to my cry, for I am in desperate need. Deliver me from my persecutors, for they are too strong for me.
7 Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.
Bring my soul out of prison, that I may give thanks to your name. The righteous will surround me, for you will be good to me.

< Zabura 142 >