< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Cantique des montées. Souviens-toi, Yahweh, de David, de toutes ses peines!
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
Il fit ce serment à Yahweh, ce vœu au Fort de Jacob:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
« Je n'entrerai pas dans la tente où j'habite, je ne monterai pas sur le lit où je repose;
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
je n'accorderai point de sommeil à mes yeux, ni d'assoupissement à mes paupières,
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
jusqu'à ce que j'aie trouvé un lieu pour Yahweh, une demeure pour le Fort de Jacob. »
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Voici, entendions-nous dire, qu'elle est à Ephrata; nous l'avons trouvée dans les champs de Jaar.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
Allons au tabernacle de Yahweh, prosternons-nous devant l'escabeau de ses pieds.
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Lève-toi, Yahweh, viens au lieu de ton repos, toi et l'arche de ta majesté!
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Que tes prêtres soient revêtus de justice, et que tes fidèles poussent des cris d'allégresse!
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
A cause de David, ton serviteur, ne repousse pas la face de ton Oint!
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
Yahweh a juré à David la vérité, il ne s'en départira pas: « C'est du fruit de tes entrailles, que je mettrai sur ton trône.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
Si tes fils gardent mon alliance, et les préceptes que je leur enseignerai, leurs fils aussi, à tout jamais, seront assis sur ton trône. »
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Car Yahweh a choisi Sion, il l'a désirée pour sa demeure.
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
« C'est le lieu de mon repos pour toujours; j'y habiterai, car je l'ai désirée.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Je répandrai de riches bénédictions sur sa subsistance, je rassasierai de pain ses pauvres.
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
Je revêtirai de salut ses prêtres, et ses fidèles pousseront des cris d'allégresse.
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
Là je ferai grandir la puissance de David, je préparerai un flambeau à mon Oint.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Je revêtirai de honte ses ennemis, et sur son front resplendira son diadème. »

< Zabura 132 >