< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
A Song of Ascents. Out of the depths I have cried to you, Yahweh.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Lord, hear my voice. Let your ears be attentive to the voice of my petitions.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If you, Yah, kept a record of sins, Lord, who could stand?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But there is forgiveness with you, therefore you are feared.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I wait for Yahweh. My soul waits. I hope in his word.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
My soul longs for the Lord more than watchmen long for the morning, more than watchmen for the morning.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israel, hope in Yahweh, for there is loving kindness with Yahweh. Abundant redemption is with him.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
He will redeem Israel from all their sins.

< Zabura 130 >