< Zabura 125 >

1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
A Song of Ascents. Those who trust in Yahweh are as Mount Zion, which can’t be moved, but remains forever.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
As the mountains surround Jerusalem, so Yahweh surrounds his people from this time forward and forever more.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
For the scepter of wickedness won’t remain over the allotment of the righteous, so that the righteous won’t use their hands to do evil.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Do good, Yahweh, to those who are good, to those who are upright in their hearts.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
But as for those who turn away to their crooked ways, Yahweh will lead them away with the workers of iniquity. Peace be on Israel.

< Zabura 125 >