< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
A Song of Ascents. In my distress, I cried to Yahweh. He answered me.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Deliver my soul, Yahweh, from lying lips, from a deceitful tongue.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
What will be given to you, and what will be done more to you, you deceitful tongue?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Sharp arrows of the mighty, with coals of juniper.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Woe is me, that I live in Meshech, that I dwell among the tents of Kedar!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
My soul has had her dwelling too long with him who hates peace.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
I am for peace, but when I speak, they are for war.

< Zabura 120 >