< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give thanks to Yahweh, for he is good, for his loving kindness endures forever.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let Israel now say that his loving kindness endures forever.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let the house of Aaron now say that his loving kindness endures forever.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Now let those who fear Yahweh say that his loving kindness endures forever.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Out of my distress, I called on Yah. Yah answered me with freedom.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Yahweh is on my side. I will not be afraid. What can man do to me?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Yahweh is on my side among those who help me. Therefore I will look in triumph at those who hate me.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
It is better to take refuge in Yahweh, than to put confidence in man.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
It is better to take refuge in Yahweh, than to put confidence in princes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
All the nations surrounded me, but in Yahweh’s name I cut them off.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They surrounded me, yes, they surrounded me. In Yahweh’s name I indeed cut them off.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They surrounded me like bees. They are quenched like the burning thorns. In Yahweh’s name I cut them off.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
You pushed me back hard, to make me fall, but Yahweh helped me.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Yah is my strength and song. He has become my salvation.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
The voice of rejoicing and salvation is in the tents of the righteous. “The right hand of Yahweh does valiantly.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
The right hand of Yahweh is exalted! The right hand of Yahweh does valiantly!”
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
I will not die, but live, and declare Yah’s works.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Yah has punished me severely, but he has not given me over to death.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Open to me the gates of righteousness. I will enter into them. I will give thanks to Yah.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
This is the gate of Yahweh; the righteous will enter into it.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
I will give thanks to you, for you have answered me, and have become my salvation.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
The stone which the builders rejected has become the cornerstone.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
This is Yahweh’s doing. It is marvelous in our eyes.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
This is the day that Yahweh has made. We will rejoice and be glad in it!
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Save us now, we beg you, Yahweh! Yahweh, we beg you, send prosperity now.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Blessed is he who comes in Yahweh’s name! We have blessed you out of Yahweh’s house.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Yahweh is God, and he has given us light. Bind the sacrifice with cords, even to the horns of the altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
You are my God, and I will give thanks to you. You are my God, I will exalt you.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Oh give thanks to Yahweh, for he is good, for his loving kindness endures forever.

< Zabura 118 >