< Zabura 11 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
For the Chief Musician. By David. In Yahweh, I take refuge. How can you say to my soul, “Flee as a bird to your mountain”?
2 Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
For, behold, the wicked bend their bows. They set their arrows on the strings, that they may shoot in darkness at the upright in heart.
3 Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
If the foundations are destroyed, what can the righteous do?
4 Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
Yahweh is in his holy temple. Yahweh is on his throne in heaven. His eyes observe. His eyes examine the children of men.
5 Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
Yahweh examines the righteous, but his soul hates the wicked and him who loves violence.
6 A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
On the wicked he will rain blazing coals; fire, sulfur, and scorching wind shall be the portion of their cup.
7 Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.
For Yahweh is righteous. He loves righteousness. The upright shall see his face.

< Zabura 11 >