< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
למנצח לדוד מזמור אלהי תהלתי אל תחרש׃
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
כי פי רשע ופי מרמה עלי פתחו דברו אתי לשון שקר׃
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
ודברי שנאה סבבוני וילחמוני חנם׃
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
תחת אהבתי ישטנוני ואני תפלה׃
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
וישימו עלי רעה תחת טובה ושנאה תחת אהבתי׃
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
הפקד עליו רשע ושטן יעמד על ימינו׃
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
בהשפטו יצא רשע ותפלתו תהיה לחטאה׃
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
יהיו ימיו מעטים פקדתו יקח אחר׃
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
יהיו בניו יתומים ואשתו אלמנה׃
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
ונוע ינועו בניו ושאלו ודרשו מחרבותיהם׃
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
ינקש נושה לכל אשר לו ויבזו זרים יגיעו׃
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
אל יהי לו משך חסד ואל יהי חונן ליתומיו׃
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
יהי אחריתו להכרית בדור אחר ימח שמם׃
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
יזכר עון אבתיו אל יהוה וחטאת אמו אל תמח׃
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
יהיו נגד יהוה תמיד ויכרת מארץ זכרם׃
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
יען אשר לא זכר עשות חסד וירדף איש עני ואביון ונכאה לבב למותת׃
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
ויאהב קללה ותבואהו ולא חפץ בברכה ותרחק ממנו׃
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
וילבש קללה כמדו ותבא כמים בקרבו וכשמן בעצמותיו׃
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
תהי לו כבגד יעטה ולמזח תמיד יחגרה׃
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
זאת פעלת שטני מאת יהוה והדברים רע על נפשי׃
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
ואתה יהוה אדני עשה אתי למען שמך כי טוב חסדך הצילני׃
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
כי עני ואביון אנכי ולבי חלל בקרבי׃
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
כצל כנטותו נהלכתי ננערתי כארבה׃
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
ברכי כשלו מצום ובשרי כחש משמן׃
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
ואני הייתי חרפה להם יראוני יניעון ראשם׃
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
עזרני יהוה אלהי הושיעני כחסדך׃
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
וידעו כי ידך זאת אתה יהוה עשיתה׃
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
יקללו המה ואתה תברך קמו ויבשו ועבדך ישמח׃
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
ילבשו שוטני כלמה ויעטו כמעיל בשתם׃
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
אודה יהוה מאד בפי ובתוך רבים אהללנו׃
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
כי יעמד לימין אביון להושיע משפטי נפשו׃

< Zabura 109 >