< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
For the Chief Musician. A Psalm by David. God of my praise, don’t remain silent,
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
for they have opened the mouth of the wicked and the mouth of deceit against me. They have spoken to me with a lying tongue.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
They have also surrounded me with words of hatred, and fought against me without a cause.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
In return for my love, they are my adversaries; but I am in prayer.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
They have rewarded me evil for good, and hatred for my love.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Set a wicked man over him. Let an adversary stand at his right hand.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
When he is judged, let him come out guilty. Let his prayer be turned into sin.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Let his days be few. Let another take his office.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Let his children be fatherless, and his wife a widow.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Let his children be wandering beggars. Let them be sought from their ruins.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Let the creditor seize all that he has. Let strangers plunder the fruit of his labor.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Let there be no one to extend kindness to him, neither let there be anyone to have pity on his fatherless children.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Let his posterity be cut off. In the generation following let their name be blotted out.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Let the iniquity of his fathers be remembered by Yahweh. Don’t let the sin of his mother be blotted out.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Let them be before Yahweh continually, that he may cut off their memory from the earth;
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
because he didn’t remember to show kindness, but persecuted the poor and needy man, the broken in heart, to kill them.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Yes, he loved cursing, and it came to him. He didn’t delight in blessing, and it was far from him.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
He clothed himself also with cursing as with his garment. It came into his inward parts like water, like oil into his bones.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Let it be to him as the clothing with which he covers himself, for the belt that is always around him.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
This is the reward of my adversaries from Yahweh, of those who speak evil against my soul.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
But deal with me, Yahweh the Lord, for your name’s sake, because your loving kindness is good, deliver me;
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
for I am poor and needy. My heart is wounded within me.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
I fade away like an evening shadow. I am shaken off like a locust.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
My knees are weak through fasting. My body is thin and lacks fat.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
I have also become a reproach to them. When they see me, they shake their head.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Help me, Yahweh, my God. Save me according to your loving kindness;
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
that they may know that this is your hand; that you, Yahweh, have done it.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
They may curse, but you bless. When they arise, they will be shamed, but your servant shall rejoice.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Let my adversaries be clothed with dishonor. Let them cover themselves with their own shame as with a robe.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
I will give great thanks to Yahweh with my mouth. Yes, I will praise him among the multitude.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
For he will stand at the right hand of the needy, to save him from those who judge his soul.

< Zabura 109 >