< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
(Af David.) Min Sjæl, lov Herren, og alt i mig love hans hellige navn!
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Min Sjæl, lov HERREN, og glem ikke alle hans Velgerninger!
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
Han, som tilgiver alle dine Misgerninger og læger alle dine Sygdomme,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
han, som udløser dit Liv fra Graven og kroner dig med Miskundhed og Barmhjertighed,
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
han, som mætter din Sjæl med godt, så du bliver ung igen som Ørnen!
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
HERREN øver Retfærdighed og Ret mod alle fortrykte.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Han lod Moses se sine Veje, Israels Børn sine Gerninger;
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
barmhjertig og nådig er HERREN, langmodig og rig på Miskundhed;
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
han går ikke bestandig i Rette, gemmer ej evigt på Vrede;
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
han handled ej med os efter vore Synder, gengældte os ikke efter vor Brøde.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Men så højt som Himlen er over Jorden, er hans Miskundhed stor over dem, der frygter ham.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Så langt som Østen er fra Vesten, har han fjernet vore Synder fra os.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Som en Fader forbarmer sig over sine Børn, forbarmer HERREN sig over dem, der frygter ham.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Thi han kender vor Skabning, han kommer i Hu, vi er Støv;
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
som Græs er Menneskets dage, han blomstrer som Markens Blomster;
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
når et Vejr farer over ham, er han ej mere, hans Sted får ham aldrig at se igen.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Men HERRENs Miskundhed varer fra Evighed og til Evighed over dem, der frygter ham, og hans Retfærd til Børnenes Børn
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
for dem, der holder hans Pagt og kommer hans Bud i Hu, så de gør derefter.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
HERREN har rejst sin Trone i Himlen, alt er hans Kongedømme underlagt.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Lov HERREN, I hans Engle, I vældige i Kraft, som gør, hvad han byder, så snart I hører hans Røst.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Lov HERREN, alle hans Hærskarer, hans Tjenere, som fuldbyrder hans Vilje.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Lov HERREN, alt, hvad han skabte, på hvert eneste Sted i hans Rige! Min Sjæl, lov HERREN!

< Zabura 103 >