< Zabura 101 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
A Psalm by David. I will sing of loving kindness and justice. To you, Yahweh, I will sing praises.
2 Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
I will be careful to live a blameless life. When will you come to me? I will walk within my house with a blameless heart.
3 Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
I will set no vile thing before my eyes. I hate the deeds of faithless men. They will not cling to me.
4 Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
A perverse heart will be far from me. I will have nothing to do with evil.
5 Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
I will silence whoever secretly slanders his neighbor. I won’t tolerate one who is arrogant and conceited.
6 Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
My eyes will be on the faithful of the land, that they may dwell with me. He who walks in a perfect way, he will serve me.
7 Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
He who practices deceit won’t dwell within my house. He who speaks falsehood won’t be established before my eyes.
8 Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.
Morning by morning, I will destroy all the wicked of the land, to cut off all the workers of iniquity from Yahweh’s city.

< Zabura 101 >