< Karin Magana 6 >

1 Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
My son, if you have become collateral for your neighbor, if you have struck your hands in pledge for a stranger,
2 in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
you are trapped by the words of your mouth; you are ensnared with the words of your mouth.
3 to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
Do this now, my son, and deliver yourself, since you have come into the hand of your neighbor. Go, humble yourself. Press your plea with your neighbor.
4 Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
Give no sleep to your eyes, nor slumber to your eyelids.
5 Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
Free yourself, like a gazelle from the hand of the hunter, like a bird from the snare of the fowler.
6 Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
Go to the ant, you sluggard. Consider her ways, and be wise;
7 Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
which having no chief, overseer, or ruler,
8 duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
provides her bread in the summer, and gathers her food in the harvest.
9 Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
How long will you sleep, sluggard? When will you arise out of your sleep?
10 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
A little sleep, a little slumber, a little folding of the hands to sleep—
11 talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
so your poverty will come as a robber, and your scarcity as an armed man.
12 Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
A worthless person, a man of iniquity, is he who walks with a perverse mouth,
13 wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
who winks with his eyes, who signals with his feet, who motions with his fingers,
14 wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
in whose heart is perverseness, who devises evil continually, who always sows discord.
15 Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
Therefore his calamity will come suddenly. He will be broken suddenly, and that without remedy.
16 Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
There are six things which Yahweh hates; yes, seven which are an abomination to him:
17 duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
arrogant eyes, a lying tongue, hands that shed innocent blood,
18 zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
a heart that devises wicked schemes, feet that are swift in running to mischief,
19 mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
a false witness who utters lies, and he who sows discord among brothers.
20 Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
My son, keep your father’s commandment, and don’t forsake your mother’s teaching.
21 Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
Bind them continually on your heart. Tie them around your neck.
22 Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
When you walk, it will lead you. When you sleep, it will watch over you. When you awake, it will talk with you.
23 Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
For the commandment is a lamp, and the law is light. Reproofs of instruction are the way of life,
24 suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
to keep you from the immoral woman, from the flattery of the wayward wife’s tongue.
25 Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
Don’t lust after her beauty in your heart, neither let her captivate you with her eyelids.
26 Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
For a prostitute reduces you to a piece of bread. The adulteress hunts for your precious life.
27 Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
Can a man scoop fire into his lap, and his clothes not be burned?
28 Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
Or can one walk on hot coals, and his feet not be scorched?
29 Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
So is he who goes in to his neighbor’s wife. Whoever touches her will not be unpunished.
30 Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
Men don’t despise a thief if he steals to satisfy himself when he is hungry,
31 Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
but if he is found, he shall restore seven times. He shall give all the wealth of his house.
32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
He who commits adultery with a woman is void of understanding. He who does it destroys his own soul.
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
He will get wounds and dishonor. His reproach will not be wiped away.
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
For jealousy arouses the fury of the husband. He won’t spare in the day of vengeance.
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.
He won’t regard any ransom, neither will he rest content, though you give many gifts.

< Karin Magana 6 >