< Karin Magana 30 >

1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
Słowa Agura, syna Jake, proroctwo tego człowieka do Itiela, do Itiela i Ukala.
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
Zaprawdę jestem najgłupszym z ludzi i nie mam ludzkiego rozumu.
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
Ani nie nauczyłem się mądrości, ani nie mam wiedzy o tym, co święty.
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
Któż wstąpił do nieba i zstąpił? Któż zebrał wiatr w swoje garście? Któż zgarnął wody do [swej] szaty? Któż utwierdził wszystkie krańce ziemi? Jakie [jest] jego imię? A jakie [jest] imię jego syna? Czy wiesz?
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Każde słowo Boga jest czyste; on [jest] tarczą dla tych, którzy mu ufają.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Nie dodawaj nic do jego słów, aby cię nie strofował i abyś nie okazał się kłamcą.
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
Proszę cię o dwie rzeczy; nie odmawiaj mi [ich], zanim umrę.
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Oddal ode mnie marność i słowo kłamliwe; nie dawaj mi ani ubóstwa, ani bogactwa; żyw mnie odpowiednim dla mnie pokarmem;
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
Abym będąc syty, nie zaparł się [ciebie] i nie mówił: Kim jest PAN? Albo zubożawszy, nie kradł i nie brał imienia mego Boga [nadaremnie].
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
Nie oczerniaj sługi przed jego panem, aby ci nie złorzeczył i byś nie okazał się winny.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
[Jest] pokolenie, które złorzeczy swemu ojcu i nie błogosławi swojej matce.
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
[Jest] pokolenie, które we własnych oczach jest czyste, lecz nie jest obmyte ze swego plugastwa.
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
[Jest] pokolenie, którego oczy są wyniosłe i powieki wzniesione.
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
[Jest] pokolenie, którego zęby [są jak] miecze, a zęby trzonowe [jak] noże, by pożreć ubogich na ziemi i nędzarzy spośród ludzi.
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
Pijawka ma dwie córki, [które mówią]: Daj, daj. Trzy są rzeczy, które nie mogą się nasycić; cztery, które nie mówią: Dość.
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
Grób, niepłodne łono, ziemia niesyta wody i ogień, [który] nie mówi: Dość. (Sheol h7585)
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
Oko, [które] wyśmiewa ojca i gardzi posłuszeństwem matce, wydziobią kruki [nad] potokami i wyjedzą orlęta.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
Trzy [są] rzeczy dla mnie zbyt zdumiewające, czterech nie znam:
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
Drogi orła w powietrzu, drogi węża na skale, drogi okrętu na środku morza i drogi mężczyzny z młodą kobietą.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
Taka [jest] droga kobiety cudzołożnej: je i obciera swoje usta, i mówi: Nie zrobiłam nic złego.
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
Pod trzema rzeczami drży ziemia, czterech nie może znieść:
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
Sługi, kiedy panuje, głupca, kiedy syci się chlebem;
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
Obmierzłej [kobiety], kiedy wychodzi za mąż, [i] służącej, kiedy dziedziczy po swojej pani.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
Cztery są rzeczy najmniejsze na ziemi, jednak mędrsze nad mędrców:
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
Mrówki, lud słaby, a jednak w lecie przygotowują pokarm;
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
Króliki, lud słaby, a jednak budują swój dom w skale;
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
Szarańcze nie mają króla, a jednak wszystkie wyruszają chmarą;
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
Pająk pracuje rękoma, a bywa w pałacach królewskich.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
Trzy są rzeczy, które poruszają się wspaniale, cztery kroczą dostojnie:
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
Lew, najsilniejszy wśród zwierząt, który przed nikim nie ustępuje;
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
Chart i kozioł, i król, przeciw któremu nikt nie powstaje.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
Jeśli głupio postąpiłeś, wynosząc się, albo jeśli pomyślałeś źle, [połóż] rękę na ustach.
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
Jak ubijanie mleka daje masło i wycieranie nosa wywołuje krew, tak kto wzbudza gniew, wszczyna kłótnię.

< Karin Magana 30 >