< Karin Magana 30 >

1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
The words of Agur the son of Jakeh, the revelation: the man says to Ithiel, to Ithiel and Ucal:
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
“Surely I am the most ignorant man, and don’t have a man’s understanding.
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
I have not learned wisdom, neither do I have the knowledge of the Holy One.
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
Who has ascended up into heaven, and descended? Who has gathered the wind in his fists? Who has bound the waters in his garment? Who has established all the ends of the earth? What is his name, and what is his son’s name, if you know?
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
“Every word of God is flawless. He is a shield to those who take refuge in him.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Don’t you add to his words, lest he reprove you, and you be found a liar.
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
“Two things I have asked of you. Don’t deny me before I die.
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Remove far from me falsehood and lies. Give me neither poverty nor riches. Feed me with the food that is needful for me,
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
lest I be full, deny you, and say, ‘Who is Yahweh?’ or lest I be poor, and steal, and so dishonor the name of my God.
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
“Don’t slander a servant to his master, lest he curse you, and you be held guilty.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
There is a generation that curses their father, and doesn’t bless their mother.
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
There is a generation that is pure in their own eyes, yet are not washed from their filthiness.
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
There is a generation, oh how lofty are their eyes! Their eyelids are lifted up.
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
There is a generation whose teeth are like swords, and their jaws like knives, to devour the poor from the earth, and the needy from among men.
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
“The leech has two daughters: ‘Give, give.’ “There are three things that are never satisfied; four that don’t say, ‘Enough!’:
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
Sheol, the barren womb, the earth that is not satisfied with water, and the fire that doesn’t say, ‘Enough!’ (Sheol h7585)
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
“The eye that mocks at his father, and scorns obedience to his mother, the ravens of the valley shall pick it out, the young eagles shall eat it.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
“There are three things which are too amazing for me, four which I don’t understand:
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
The way of an eagle in the air, the way of a serpent on a rock, the way of a ship in the middle of the sea, and the way of a man with a maiden.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
“So is the way of an adulterous woman: She eats and wipes her mouth, and says, ‘I have done nothing wrong.’
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
“For three things the earth trembles, and under four, it can’t bear up:
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
For a servant when he is king, a fool when he is filled with food,
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
for an unloved woman when she is married, and a servant who is heir to her mistress.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
“There are four things which are little on the earth, but they are exceedingly wise:
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
The ants are not a strong people, yet they provide their food in the summer.
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
The hyraxes are but a feeble folk, yet make they their houses in the rocks.
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
The locusts have no king, yet they advance in ranks.
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
You can catch a lizard with your hands, yet it is in kings’ palaces.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
“There are three things which are stately in their march, four which are stately in going:
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
The lion, which is mightiest among animals, and doesn’t turn away for any;
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
the greyhound; the male goat; and the king against whom there is no rising up.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
“If you have done foolishly in lifting up yourself, or if you have thought evil, put your hand over your mouth.
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
For as the churning of milk produces butter, and the wringing of the nose produces blood, so the forcing of wrath produces strife.”

< Karin Magana 30 >