< Karin Magana 22 >

1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
A good name is more desirable than great riches, and loving favor is better than silver and gold.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
The rich and the poor have this in common: Yahweh is the maker of them all.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
A prudent man sees danger and hides himself; but the simple pass on, and suffer for it.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
The result of humility and the fear of Yahweh is wealth, honor, and life.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Thorns and snares are in the path of the wicked; whoever guards his soul stays far from them.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Train up a child in the way he should go, and when he is old he will not depart from it.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
The rich rule over the poor. The borrower is servant to the lender.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
He who sows wickedness reaps trouble, and the rod of his fury will be destroyed.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
He who has a generous eye will be blessed, for he shares his food with the poor.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Drive out the mocker, and strife will go out; yes, quarrels and insults will stop.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
He who loves purity of heart and speaks gracefully is the king’s friend.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Yahweh’s eyes watch over knowledge, but he frustrates the words of the unfaithful.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
The sluggard says, “There is a lion outside! I will be killed in the streets!”
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
The mouth of an adulteress is a deep pit. He who is under Yahweh’s wrath will fall into it.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
Folly is bound up in the heart of a child; the rod of discipline drives it far from him.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Whoever oppresses the poor for his own increase and whoever gives to the rich, both come to poverty.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Turn your ear, and listen to the words of the wise. Apply your heart to my teaching.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
For it is a pleasant thing if you keep them within you, if all of them are ready on your lips.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
I teach you today, even you, so that your trust may be in Yahweh.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
Haven’t I written to you thirty excellent things of counsel and knowledge,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
To teach you truth, reliable words, to give sound answers to the ones who sent you?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Don’t exploit the poor because he is poor; and don’t crush the needy in court;
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
for Yahweh will plead their case, and plunder the life of those who plunder them.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Don’t befriend a hot-tempered man. Don’t associate with one who harbors anger,
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
lest you learn his ways and ensnare your soul.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Don’t you be one of those who strike hands, of those who are collateral for debts.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
If you don’t have means to pay, why should he take away your bed from under you?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Don’t move the ancient boundary stone which your fathers have set up.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Do you see a man skilled in his work? He will serve kings. He won’t serve obscure men.

< Karin Magana 22 >