< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
My son, if you will receive my words, and store up my commandments within you,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
so as to turn your ear to wisdom, and apply your heart to understanding;
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
yes, if you call out for discernment, and lift up your voice for understanding;
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
if you seek her as silver, and search for her as for hidden treasures;
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
then you will understand the fear of Yahweh, and find the knowledge of God.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
For Yahweh gives wisdom. Out of his mouth comes knowledge and understanding.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
He lays up sound wisdom for the upright. He is a shield to those who walk in integrity,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
that he may guard the paths of justice, and preserve the way of his saints.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Then you will understand righteousness and justice, equity and every good path.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
For wisdom will enter into your heart. Knowledge will be pleasant to your soul.
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Discretion will watch over you. Understanding will keep you,
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
to deliver you from the way of evil, from the men who speak perverse things,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
who forsake the paths of uprightness, to walk in the ways of darkness,
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
who rejoice to do evil, and delight in the perverseness of evil,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
who are crooked in their ways, and wayward in their paths,
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
to deliver you from the strange woman, even from the foreigner who flatters with her words,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
who forsakes the friend of her youth, and forgets the covenant of her God;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
for her house leads down to death, her paths to the departed spirits.
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
None who go to her return again, neither do they attain to the paths of life.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Therefore walk in the way of good men, and keep the paths of the righteous.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
For the upright will dwell in the land. The perfect will remain in it.
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
But the wicked will be cut off from the land. The treacherous will be rooted out of it.

< Karin Magana 2 >