< Karin Magana 11 >

1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
A false balance is an abomination to Yahweh, but accurate weights are his delight.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
When pride comes, then comes shame, but with humility comes wisdom.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
The integrity of the upright shall guide them, but the perverseness of the treacherous shall destroy them.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
Riches don’t profit in the day of wrath, but righteousness delivers from death.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
The righteousness of the blameless will direct his way, but the wicked shall fall by his own wickedness.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
The righteousness of the upright shall deliver them, but the unfaithful will be trapped by evil desires.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
When a wicked man dies, hope perishes, and expectation of power comes to nothing.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
A righteous person is delivered out of trouble, and the wicked takes his place.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
With his mouth the godless man destroys his neighbor, but the righteous will be delivered through knowledge.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
When it goes well with the righteous, the city rejoices. When the wicked perish, there is shouting.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
By the blessing of the upright, the city is exalted, but it is overthrown by the mouth of the wicked.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
One who despises his neighbor is void of wisdom, but a man of understanding holds his peace.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
One who brings gossip betrays a confidence, but one who is of a trustworthy spirit is one who keeps a secret.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Where there is no wise guidance, the nation falls, but in the multitude of counselors there is victory.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
He who is collateral for a stranger will suffer for it, but he who refuses pledges of collateral is secure.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
A gracious woman obtains honor, but violent men obtain riches.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
The merciful man does good to his own soul, but he who is cruel troubles his own flesh.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
Wicked people earn deceitful wages, but one who sows righteousness reaps a sure reward.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
He who is truly righteous gets life. He who pursues evil gets death.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
Those who are perverse in heart are an abomination to Yahweh, but those whose ways are blameless are his delight.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
Most certainly, the evil man will not be unpunished, but the offspring of the righteous will be delivered.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
Like a gold ring in a pig’s snout, is a beautiful woman who lacks discretion.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
The desire of the righteous is only good. The expectation of the wicked is wrath.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
There is one who scatters, and increases yet more. There is one who withholds more than is appropriate, but gains poverty.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
The liberal soul shall be made fat. He who waters shall be watered also himself.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
People curse someone who withholds grain, but blessing will be on the head of him who sells it.
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
He who diligently seeks good seeks favor, but he who searches after evil, it shall come to him.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
He who trusts in his riches will fall, but the righteous shall flourish as the green leaf.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
He who troubles his own house shall inherit the wind. The foolish shall be servant to the wise of heart.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
The fruit of the righteous is a tree of life. He who is wise wins souls.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Behold, the righteous shall be repaid in the earth, how much more the wicked and the sinner!

< Karin Magana 11 >