< Filibbiyawa 4 >

1 Saboda haka’yan’uwana, ku da nake ƙauna, nake kuma marmarin ganinku, ku da kuke farin cikina da kuma rawanina, ku dāge ga Ubangiji, ya ku ƙaunatattuna!
NOLAILA hoi, e na hoahanau o'u i alohaia, a i makemake nui ia, o kuu olioli a me kuu leialii; pela e kupaa ai oukou iloko o ka Haku, e na mea i alohaia.
2 Ina roƙon Yuwodiya ina kuma roƙon Sintike, su yi zaman lafiya da juna saboda su na Ubangiji ne.
Ke noi aku nei au ia Euodia, ke noi aku nei hoi au ia Sunetuke, i hookahi ko laua manao iloko o ka Haku.
3 I, ina kuma roƙonka, abokin famata, ka taimaki matan nan waɗanda suka yi fama aikin bishara tare da ni, haka ma Kilemen da kuma sauran abokan aikina, waɗanda sunayensu suna cikin littafin rai.
Ke noi aku nei hoi au ia oe kekahi, e ka hoalawehana io, e kokua aku oe ia mau wahine, i hooikaika pu me au ma ka euanelio, a me Kelemeneto hoi, a me o'u mau hoalawehana e ae, aia no maloko o ka buke ola ko lakou mau inoa.
4 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji kullum. Ina sāke gaya muku ku yi farin ciki!
E hauoli mau oukou i ka Haku; ke olelo hou aku nei hoi au, e hauoli oukou.
5 Bari kowa yă kasance da sauƙinkai. Ubangiji ya yi kusan zuwa.
I hoikeia hoi ko oukou akahai i na kanaka a pau. Ua kokoke mai ka Haku.
6 Kada ku damu game da kome sai dai a cikin abu duka, ku gabatar da roƙe-roƙenku ga Allah ta wurin addu’a da roƙo, tare da godiya.
Mai manao nui oukou i kekahi mea; aka, i na mea a pau e hoike aku i ko oukou makemake i ke Akua ma ka pule, a me ka noi aku, a me ka hoomaikai aku.
7 Salamar Allah, wadda ta wuce dukan fahimta, za tă tsai da zukatanku da tunaninku cikin Kiristi Yesu.
A o ka maluhia o ke Akua, ka mea i oi aku i ko ke kanaka manao a pau, e hoomalu mai i ko oukou naau a me ko oukou manao ma o Kristo Iesu la.
8 A ƙarshe,’yan’uwa, duk abin da yake na gaskiya, duk abin da yake na girmamawa, duk abin da yake daidai, duk abin da yake da tsarki, duk abin da yake kyakkyawa, duk abin da yake na sha’awa, in ma wani abu mafifici ne, ko ya cancanci yabo, ku yi tunani a kan irin abubuwan nan.
Eia hoi e na hoahanau, o na mea oiaio, na mea maikai, na mea pono, na mea hala ole, na mea lokomaikai, na mea lono maikai ia; ina he mea kupono, ina hoi he mea e hoomaikaiia'i, e noonoo iho oukou ia mau mea.
9 Duk abin da kuka koya ko kuka karɓa ko kuka ji daga wurina, ko kuka gani a cikina, ku yi aiki da shi. Allah na salama kuma zai kasance tare da ku.
O na mea a oukou i aoia'i, i loaa hoi, i lohe a i ike hoi ia'u, o keia ka oukou e hana'i; a me oukou hoi ke Akua ka mea e malu ai.
10 Na yi farin ciki sosai ga Ubangiji don yanzu kun sāke nuna kun kula da ni. Ko da yake dā ma kun kula da ni sai dai ba ku sami dama ku nuna mini ba.
Ua olioli nui au i ka Haku, no ka mea, ua kupu hou mai ko oukou manao e kokua ia'u; malaila no oukou i manao ai, aka, aole a oukou mea e hiki ai.
11 Ba na faɗin haka domin ina cikin bukata, gama na koya yadda zan gamsu a cikin kowane hali.
Aole au i olelo pela no ka nele; no ka mea, ua aoia hoi au e oluolu iho i na mea a pau i loaa ia'u.
12 Na san mene ne zaman rashi, na kuma san mene ne zaman samu. Zan iya zama cikin kowane hali, ko cikin ƙoshi ko cikin yunwa, ko cikin yalwa ko kuma cikin fatara.
Ua ike hoi au i ka noho ilihune, a me ka noho lako: i na wahi a pau, a i na mea a pau, ua aoia mai la au e noho maona a e noho pololi, e noho lako a e noho nele.
13 Ina iya yin kome ta wurin wannan wanda yake ba ni ƙarfi.
E hiki no ia'u na mea a pau, ke kokua mai o Kristo ia'u.
14 Duk da haka kun kyauta da kuka yi tarayya da ni cikin wahalolina.
Aka hoi, ua hana pono mai oukou, i ko oukou manawalea ana mai ia'u i ko'u popilikia.
15 Ban da haka, kamar yadda ku Filibbiyawa kuka sani, a farkon kwanakin da kuka ji bishara, sa’ad da na tashi daga Makidoniya, babu wata ikkilisiyar da tă yi tarayya da ni a fannin bayarwa da karɓa, sai ku kaɗai;
E ko Pilipi, ua ike no oukou, i ka wa kinohou o ka euanelio, ia'u i haalele ai ia Makedonia, aole kekahi ekalesia e ae i launa mai ia'u i ka haawi ana a i ka lawe ana, o oukou wale no.
16 gama ko sa’ad da nake a Tessalonika ma, kun aiko mini da taimako sau da sau sa’ad da nake cikin bukata.
No ka mea, a i Tesalouike hookahi a elua hoi o ko oukou hoouka ana mai i ka mea e pono ai kuu nele.
17 Ba cewa ina neman kyauta ba ne, sai dai ina neman abin da za a ƙara a kan ribarku.
Aole ka makana ka'u e imi nei; aka, ke imi nei au i ka hua e nui ai ko oukou pono.
18 An biya ni duka, biyan da ya wuce misali. Bukatata ta biya, da yake na karɓi kyautarku da kuka aiko ta hannun Afaforiditus. Baiwa mai ƙanshi, hadaya abar karɓa, mai faranta wa Allah rai.
A ia'u na mea he nui, a ua lako hoi: ua piha au i ka oukou mau mea i loaa mai ma o Epaperodito la, he mea ala oluolu, he mohai hooluolu, i maliuia mai hoi e ke Akua.
19 Allahna kuma zai biya dukan bukatunku bisa ga ɗaukakar wadatarsa cikin Kiristi Yesu.
Aka, e haawi mai ana ko'u Akua i na mea a pau e pono ai oukou, no kona waiwai i kahi nani ma o Kristo Iesu la.
20 Ɗaukaka ta tabbata ga Allahnmu da Ubanmu har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
A i ke Akua ko kakou Makua ka hoonani mau loa ia i ke ao pau ole. Amene. (aiōn g165)
21 Ku gai da dukan tsarkaka cikin Kiristi Yesu.’Yan’uwan da suke tare da ni suna gaishe ku.
E uwe aku i na haipule a pau iloko o Kristo Iesu. Ke uwe aku nei na hoahanau me au ia oukou.
22 Dukan tsarkaka suna gaishe ku, musamman waɗanda suke na gidan Kaisar.
Ke uwe aku nei na haipule a pau ia oukou, o lakou hoi no na ohua o Kaisara.
23 Alherin Ubangiji Yesu Kiristi yă kasance da ruhunku. Amin.
O ke aloha o ko kakou Haku o Iesu Kristo me oukou a pau. Amene.

< Filibbiyawa 4 >