< Ƙidaya 25 >

1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
And Israel abode in Shittim, and the people began to commit whoredom with the daughters of Moab.
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
And they called the people unto the sacrifices of their gods: and the people did eat, and bowed down to their gods.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
And Israel joined himself unto Baal-peor: and the anger of the LORD was kindled against Israel.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
And the LORD said unto Moses, Take all the heads of the people, and hang them up before the LORD against the sun, that the fierce anger of the LORD may be turned away from Israel.
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
And Moses said unto the judges of Israel, Slay ye every one his men that were joined unto Baal-peor.
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
And, behold, one of the children of Israel came and brought unto his brethren a Midianitish woman in the sight of Moses, and in the sight of all the congregation of the children of Israel, who [were] weeping [before] the door of the tabernacle of the congregation.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
And when Phinehas, the son of Eleazar, the son of Aaron the priest, saw [it], he rose up from among the congregation, and took a javelin in his hand;
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
And he went after the man of Israel into the tent, and thrust both of them through, the man of Israel, and the woman through her belly. So the plague was stayed from the children of Israel.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
And those that died in the plague were twenty and four thousand.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
Phinehas, the son of Eleazar, the son of Aaron the priest, hath turned my wrath away from the children of Israel, while he was zealous for my sake among them, that I consumed not the children of Israel in my jealousy.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
Wherefore say, Behold, I give unto him my covenant of peace:
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
And he shall have it, and his seed after him, [even] the covenant of an everlasting priesthood; because he was zealous for his God, and made an atonement for the children of Israel.
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
Now the name of the Israelite that was slain, [even] that was slain with the Midianitish woman, [was] Zimri, the son of Salu, a prince of a chief house among the Simeonites.
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
And the name of the Midianitish woman that was slain [was] Cozbi, the daughter of Zur; he [was] head over a people, [and] of a chief house in Midian.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
Vex the Midianites, and smite them:
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
For they vex you with their wiles, wherewith they have beguiled you in the matter of Peor, and in the matter of Cozbi, the daughter of a prince of Midian, their sister, which was slain in the day of the plague for Peor’s sake.

< Ƙidaya 25 >