< Ƙidaya 15 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh spoke to Moses, saying,
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
“Speak to the children of Israel, and tell them, ‘When you have come into the land of your habitations, which I give to you,
3 kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
and will make an offering by fire to Yahweh—a burnt offering, or a sacrifice, to accomplish a vow, or as a free will offering, or in your set feasts, to make a pleasant aroma to Yahweh, of the herd, or of the flock—
4 sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
then he who offers his offering shall offer to Yahweh a meal offering of one tenth of an ephah of fine flour mixed with one fourth of a hin of oil.
5 Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
You shall prepare wine for the drink offering, one fourth of a hin, with the burnt offering or for the sacrifice, for each lamb.
6 “‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
“‘For a ram, you shall prepare for a meal offering two tenths of an ephah of fine flour mixed with the third part of a hin of oil;
7 da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
and for the drink offering you shall offer the third part of a hin of wine, of a pleasant aroma to Yahweh.
8 “‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
When you prepare a bull for a burnt offering or for a sacrifice, to accomplish a vow, or for peace offerings to Yahweh,
9 sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
then he shall offer with the bull a meal offering of three tenths of an ephah of fine flour mixed with half a hin of oil;
10 A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
and you shall offer for the drink offering half a hin of wine, for an offering made by fire, of a pleasant aroma to Yahweh.
11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
Thus it shall be done for each bull, for each ram, for each of the male lambs, or of the young goats.
12 Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
According to the number that you shall prepare, so you shall do to everyone according to their number.
13 “‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
“‘All who are native-born shall do these things in this way, in offering an offering made by fire, of a pleasant aroma to Yahweh.
14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
If a stranger lives as a foreigner with you, or whoever may be among you throughout your generations, and will offer an offering made by fire, of a pleasant aroma to Yahweh, as you do, so he shall do.
15 Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
For the assembly, there shall be one statute for you and for the stranger who lives as a foreigner, a statute forever throughout your generations. As you are, so the foreigner shall be before Yahweh.
16 Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
One law and one ordinance shall be for you and for the stranger who lives as a foreigner with you.’”
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh spoke to Moses, saying,
18 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
“Speak to the children of Israel, and tell them, ‘When you come into the land where I bring you,
19 kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
then it shall be that when you eat of the bread of the land, you shall offer up a wave offering to Yahweh.
20 Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
Of the first of your dough you shall offer up a cake for a wave offering. As the wave offering of the threshing floor, so you shall heave it.
21 A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
Of the first of your dough, you shall give to Yahweh a wave offering throughout your generations.
22 “‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
“‘When you err, and don’t observe all these commandments which Yahweh has spoken to Moses—
23 ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
even all that Yahweh has commanded you by Moses, from the day that Yahweh gave commandment and onward throughout your generations—
24 in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
then it shall be, if it was done unwittingly, without the knowledge of the congregation, that all the congregation shall offer one young bull for a burnt offering, for a pleasant aroma to Yahweh, with its meal offering and its drink offering, according to the ordinance, and one male goat for a sin offering.
25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
The priest shall make atonement for all the congregation of the children of Israel, and they shall be forgiven; for it was an error, and they have brought their offering, an offering made by fire to Yahweh, and their sin offering before Yahweh, for their error.
26 Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
All the congregation of the children of Israel shall be forgiven, as well as the stranger who lives as a foreigner among them; for with regard to all the people, it was done unwittingly.
27 “‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
“‘If a person sins unwittingly, then he shall offer a female goat a year old for a sin offering.
28 Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
The priest shall make atonement for the soul who errs when he sins unwittingly before Yahweh. He shall make atonement for him; and he shall be forgiven.
29 Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
You shall have one law for him who does anything unwittingly, for him who is native-born among the children of Israel, and for the stranger who lives as a foreigner among them.
30 “‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
“‘But the soul who does anything with a high hand, whether he is native-born or a foreigner, blasphemes Yahweh. That soul shall be cut off from among his people.
31 gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
Because he has despised Yahweh’s word, and has broken his commandment, that soul shall be utterly cut off. His iniquity shall be on him.’”
32 Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
While the children of Israel were in the wilderness, they found a man gathering sticks on the Sabbath day.
33 Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
Those who found him gathering sticks brought him to Moses and Aaron, and to all the congregation.
34 sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
They put him in custody, because it had not been declared what should be done to him.
35 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
Yahweh said to Moses, “The man shall surely be put to death. All the congregation shall stone him with stones outside of the camp.”
36 Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
All the congregation brought him outside of the camp, and stoned him to death with stones, as Yahweh commanded Moses.
37 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh spoke to Moses, saying,
38 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
“Speak to the children of Israel, and tell them that they should make themselves fringes on the borders of their garments throughout their generations, and that they put on the fringe of each border a cord of blue.
39 Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
It shall be to you for a fringe, that you may see it, and remember all Yahweh’s commandments, and do them; and that you don’t follow your own heart and your own eyes, after which you used to play the prostitute;
40 Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
so that you may remember and do all my commandments, and be holy to your God.
41 Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
I am Yahweh your God, who brought you out of the land of Egypt, to be your God: I am Yahweh your God.”

< Ƙidaya 15 >