< Ƙidaya 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh spoke to Moses, saying,
2 “Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
“Send men, that they may spy out the land of Canaan, which I give to the children of Israel. Of every tribe of their fathers, you shall send a man, every one a prince among them.”
3 Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
Moses sent them from the wilderness of Paran according to the commandment of Yahweh. All of them were men who were heads of the children of Israel.
4 Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
These were their names: Of the tribe of Reuben, Shammua the son of Zaccur.
5 Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
Of the tribe of Simeon, Shaphat the son of Hori.
6 Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
Of the tribe of Judah, Caleb the son of Jephunneh.
7 Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
Of the tribe of Issachar, Igal the son of Joseph.
8 Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
Of the tribe of Ephraim, Hoshea the son of Nun.
9 daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
Of the tribe of Benjamin, Palti the son of Raphu.
10 Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
Of the tribe of Zebulun, Gaddiel the son of Sodi.
11 Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
Of the tribe of Joseph, of the tribe of Manasseh, Gaddi the son of Susi.
12 Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
Of the tribe of Dan, Ammiel the son of Gemalli.
13 Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
Of the tribe of Asher, Sethur the son of Michael.
14 Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
Of the tribe of Naphtali, Nahbi the son of Vophsi.
15 Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
Of the tribe of Gad, Geuel the son of Machi.
16 Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
These are the names of the men who Moses sent to spy out the land. Moses called Hoshea the son of Nun Joshua.
17 Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
Moses sent them to spy out the land of Canaan, and said to them, “Go up this way by the South, and go up into the hill country.
18 Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
See the land, what it is; and the people who dwell therein, whether they are strong or weak, whether they are few or many;
19 Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
and what the land is that they dwell in, whether it is good or bad; and what cities they are that they dwell in, whether in camps, or in strongholds;
20 Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
and what the land is, whether it is fertile or poor, whether there is wood therein, or not. Be courageous, and bring some of the fruit of the land.” Now the time was the time of the first-ripe grapes.
21 Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
So they went up, and spied out the land from the wilderness of Zin to Rehob, to the entrance of Hamath.
22 Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
They went up by the South, and came to Hebron; and Ahiman, Sheshai, and Talmai, the children of Anak, were there. (Now Hebron was built seven years before Zoan in Egypt.)
23 Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
They came to the valley of Eshcol, and cut down from there a branch with one cluster of grapes, and they bore it on a staff between two. They also brought some of the pomegranates and figs.
24 Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
That place was called the valley of Eshcol, because of the cluster which the children of Israel cut down from there.
25 A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
They returned from spying out the land at the end of forty days.
26 Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
They went and came to Moses, to Aaron, and to all the congregation of the children of Israel, to the wilderness of Paran, to Kadesh; and brought back word to them and to all the congregation. They showed them the fruit of the land.
27 Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
They told him, and said, “We came to the land where you sent us. Surely it flows with milk and honey, and this is its fruit.
28 Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
However, the people who dwell in the land are strong, and the cities are fortified and very large. Moreover, we saw the children of Anak there.
29 Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
Amalek dwells in the land of the South. The Hittite, the Jebusite, and the Amorite dwell in the hill country. The Canaanite dwells by the sea, and along the side of the Jordan.”
30 Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
Caleb stilled the people before Moses, and said, “Let’s go up at once, and possess it; for we are well able to overcome it!”
31 Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
But the men who went up with him said, “We aren’t able to go up against the people; for they are stronger than we.”
32 Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
They brought up an evil report of the land which they had spied out to the children of Israel, saying, “The land, through which we have gone to spy it out, is a land that eats up its inhabitants; and all the people who we saw in it are men of great stature.
33 Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”
There we saw the Nephilim, the sons of Anak, who come from the Nephilim. We were in our own sight as grasshoppers, and so we were in their sight.”

< Ƙidaya 13 >