< Ƙidaya 12 >

1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
Or Marie et Aaron parlèrent contre Moïse, au sujet de la femme éthiopienne qu'il avait prise; car il avait pris une femme éthiopienne.
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
Et ils dirent: L'Éternel n'a-t-il parlé que par Moïse seul? N'a-t-il point aussi parlé par nous? Et l'Éternel l'entendit.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
Or, Moïse était un homme fort doux, plus qu'aucun homme qui soit sur la terre.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
Et l'Éternel dit soudain à Moïse, à Aaron et à Marie: Sortez, vous trois, vers le tabernacle d'assignation. Et ils y allèrent tous trois.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
Et l'Éternel descendit dans la colonne de nuée, et se tint à l'entrée du tabernacle; puis il appela Aaron et Marie; et ils vinrent tous deux.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
Et il dit: Écoutez bien mes paroles. S'il y a parmi vous un prophète, moi, l'Éternel, je me fais connaître à lui en vision, je lui parle en songe.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Il n'en est pas ainsi de mon serviteur Moïse, qui est fidèle dans toute ma maison;
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
Je parle avec lui bouche à bouche, et en apparition, et non en énigmes, et il contemple l'image de l'Éternel. Pourquoi donc n'avez-vous pas craint de parler contre mon serviteur, contre Moïse?
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
Ainsi la colère de l'Éternel s'embrasa contre eux; et il s'en alla,
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
Et la nuée se retira de dessus le tabernacle. Et voici, Marie était frappée de lèpre, et blanche comme la neige; Aaron se tourna vers Marie, et voici, elle était lépreuse.
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
Alors Aaron dit à Moïse: Ah! mon seigneur, je te prie, ne mets point sur nous le péché que nous avons follement commis, et par lequel nous avons péché.
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Je te prie, qu'elle ne soit point comme l'enfant mort, dont la chair est à demi-consumée, quand il sort du sein de sa mère.
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
Alors Moïse cria à l'Éternel, en disant: O Dieu, je te prie, guéris-la, je te prie!
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
Et l'Éternel répondit à Moïse: Si son père lui avait craché au visage, ne serait-elle pas couverte de honte pendant sept jours? Qu'elle demeure enfermée sept jours, hors du camp, et après cela elle y sera reçue.
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
Ainsi Marie fut enfermée sept jours hors du camp; et le peuple ne partit point, jusqu'à ce que Marie y eût été reçue.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Après cela, le peuple partit de Hatséroth, et ils campèrent au désert de Paran.

< Ƙidaya 12 >