< Ƙidaya 10 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh spoke to Moses, saying,
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
“Make two trumpets of silver. You shall make them of beaten work. You shall use them for the calling of the congregation and for the journeying of the camps.
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
When they blow them, all the congregation shall gather themselves to you at the door of the Tent of Meeting.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
If they blow just one, then the princes, the heads of the thousands of Israel, shall gather themselves to you.
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
When you blow an alarm, the camps that lie on the east side shall go forward.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
When you blow an alarm the second time, the camps that lie on the south side shall go forward. They shall blow an alarm for their journeys.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
But when the assembly is to be gathered together, you shall blow, but you shall not sound an alarm.
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
“The sons of Aaron, the priests, shall blow the trumpets. This shall be to you for a statute forever throughout your generations.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
When you go to war in your land against the adversary who oppresses you, then you shall sound an alarm with the trumpets. Then you will be remembered before Yahweh your God, and you will be saved from your enemies.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
“Also in the day of your gladness, and in your set feasts, and in the beginnings of your months, you shall blow the trumpets over your burnt offerings, and over the sacrifices of your peace offerings; and they shall be to you for a memorial before your God. I am Yahweh your God.”
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
In the second year, in the second month, on the twentieth day of the month, the cloud was taken up from over the tabernacle of the covenant.
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
The children of Israel went forward on their journeys out of the wilderness of Sinai; and the cloud stayed in the wilderness of Paran.
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
They first went forward according to the commandment of Yahweh by Moses.
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
First, the standard of the camp of the children of Judah went forward according to their armies. Nahshon the son of Amminadab was over his army.
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
Nethanel the son of Zuar was over the army of the tribe of the children of Issachar.
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
Eliab the son of Helon was over the army of the tribe of the children of Zebulun.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
The tabernacle was taken down; and the sons of Gershon and the sons of Merari, who bore the tabernacle, went forward.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
The standard of the camp of Reuben went forward according to their armies. Elizur the son of Shedeur was over his army.
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
Shelumiel the son of Zurishaddai was over the army of the tribe of the children of Simeon.
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
Eliasaph the son of Deuel was over the army of the tribe of the children of Gad.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
The Kohathites set forward, bearing the sanctuary. The others set up the tabernacle before they arrived.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
The standard of the camp of the children of Ephraim set forward according to their armies. Elishama the son of Ammihud was over his army.
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
Gamaliel the son of Pedahzur was over the army of the tribe of the children of Manasseh.
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
Abidan the son of Gideoni was over the army of the tribe of the children of Benjamin.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
The standard of the camp of the children of Dan, which was the rear guard of all the camps, set forward according to their armies. Ahiezer the son of Ammishaddai was over his army.
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
Pagiel the son of Ochran was over the army of the tribe of the children of Asher.
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
Ahira the son of Enan was over the army of the tribe of the children of Naphtali.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
Thus were the travels of the children of Israel according to their armies; and they went forward.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
Moses said to Hobab, the son of Reuel the Midianite, Moses’ father-in-law, “We are journeying to the place of which Yahweh said, ‘I will give it to you.’ Come with us, and we will treat you well; for Yahweh has spoken good concerning Israel.”
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
He said to him, “I will not go; but I will depart to my own land, and to my relatives.”
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
Moses said, “Don’t leave us, please; because you know how we are to encamp in the wilderness, and you can be our eyes.
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
It shall be, if you go with us—yes, it shall be—that whatever good Yahweh does to us, we will do the same to you.”
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
They set forward from the Mount of Yahweh three days’ journey. The ark of Yahweh’s covenant went before them three days’ journey, to seek out a resting place for them.
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
The cloud of Yahweh was over them by day, when they set forward from the camp.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
When the ark went forward, Moses said, “Rise up, Yahweh, and let your enemies be scattered! Let those who hate you flee before you!”
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
When it rested, he said, “Return, Yahweh, to the ten thousands of the thousands of Israel.”

< Ƙidaya 10 >