< Nehemiya 7 >

1 Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
Now when the wall was built and I had set up the doors, and the gatekeepers and the singers and the Levites were appointed,
2 Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
I put my brother Hanani, and Hananiah the governor of the fortress, in charge of Jerusalem; for he was a faithful man and feared God above many.
3 Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
I said to them, “Don’t let the gates of Jerusalem be opened until the sun is hot; and while they stand guard, let them shut the doors, and you bar them; and appoint watches of the inhabitants of Jerusalem, everyone in his watch, with everyone near his house.”
4 Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
Now the city was wide and large; but the people were few therein, and the houses were not built.
5 Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
My God put into my heart to gather together the nobles, and the rulers, and the people, that they might be listed by genealogy. I found the book of the genealogy of those who came up at the first, and I found this written in it:
6 Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
These are the children of the province who went up out of the captivity of those who had been carried away, whom Nebuchadnezzar the king of Babylon had carried away, and who returned to Jerusalem and to Judah, everyone to his city,
7 Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
who came with Zerubbabel, Jeshua, Nehemiah, Azariah, Raamiah, Nahamani, Mordecai, Bilshan, Mispereth, Bigvai, Nehum, and Baanah. The number of the men of the people of Israel:
8 Zuriyar Farosh mutum 2,172
The children of Parosh: two thousand one hundred seventy-two.
9 ta Shefatiya 372
The children of Shephatiah: three hundred seventy-two.
10 ta Ara 652
The children of Arah: six hundred fifty-two.
11 ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
The children of Pahathmoab, of the children of Jeshua and Joab: two thousand eight hundred eighteen.
12 ta Elam 1,254
The children of Elam: one thousand two hundred fifty-four.
13 ta Zattu 845
The children of Zattu: eight hundred forty-five.
14 ta Zakkai 760
The children of Zaccai: seven hundred sixty.
15 ta Binnuyi 648
The children of Binnui: six hundred forty-eight.
16 ta Bebai 628
The children of Bebai: six hundred twenty-eight.
17 ta Azgad 2,322
The children of Azgad: two thousand three hundred twenty-two.
18 ta Adonikam 667
The children of Adonikam: six hundred sixty-seven.
19 ta Bigwai 2,067
The children of Bigvai: two thousand sixty-seven.
20 ta Adin 655
The children of Adin: six hundred fifty-five.
21 ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
The children of Ater: of Hezekiah, ninety-eight.
22 ta Hashum 328
The children of Hashum: three hundred twenty-eight.
23 ta Bezai 324
The children of Bezai: three hundred twenty-four.
24 ta Harif 112
The children of Hariph: one hundred twelve.
25 ta Gibeyon 95.
The children of Gibeon: ninety-five.
26 Mutanen Betlehem da na Netofa 188
The men of Bethlehem and Netophah: one hundred eighty-eight.
27 na Anatot 128
The men of Anathoth: one hundred twenty-eight.
28 na Bet-Azmawet 42
The men of Beth Azmaveth: forty-two.
29 na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
The men of Kiriath Jearim, Chephirah, and Beeroth: seven hundred forty-three.
30 na Rama da na Geba 621
The men of Ramah and Geba: six hundred twenty-one.
31 na Mikmash 122
The men of Michmas: one hundred twenty-two.
32 na Betel da na Ai 123
The men of Bethel and Ai: one hundred twenty-three.
33 na ɗayan Nebo 52
The men of the other Nebo: fifty-two.
34 na ɗayan Elam 1,254
The children of the other Elam: one thousand two hundred fifty-four.
35 na Harim 2 320
The children of Harim: three hundred twenty.
36 na Yeriko 345
The children of Jericho: three hundred forty-five.
37 na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
The children of Lod, Hadid, and Ono: seven hundred twenty-one.
38 na Sena’a 3,930.
The children of Senaah: three thousand nine hundred thirty.
39 Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
The priests: The children of Jedaiah, of the house of Jeshua: nine hundred seventy-three.
40 ta Immer 1,052
The children of Immer: one thousand fifty-two.
41 ta Fashhur 1,247
The children of Pashhur: one thousand two hundred forty-seven.
42 ta Harim 1,017.
The children of Harim: one thousand seventeen.
43 Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
The Levites: the children of Jeshua, of Kadmiel, of the children of Hodevah: seventy-four.
44 Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
The singers: the children of Asaph: one hundred forty-eight.
45 Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
The gatekeepers: the children of Shallum, the children of Ater, the children of Talmon, the children of Akkub, the children of Hatita, the children of Shobai: one hundred thirty-eight.
46 Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
The temple servants: the children of Ziha, the children of Hasupha, the children of Tabbaoth,
47 da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
the children of Keros, the children of Sia, the children of Padon,
48 da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
the children of Lebana, the children of Hagaba, the children of Salmai,
49 da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
the children of Hanan, the children of Giddel, the children of Gahar,
50 da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
the children of Reaiah, the children of Rezin, the children of Nekoda,
51 da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
the children of Gazzam, the children of Uzza, the children of Paseah,
52 da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
the children of Besai, the children of Meunim, the children of Nephushesim,
53 da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
the children of Bakbuk, the children of Hakupha, the children of Harhur,
54 da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
the children of Bazlith, the children of Mehida, the children of Harsha,
55 da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
the children of Barkos, the children of Sisera, the children of Temah,
56 da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
the children of Neziah, and the children of Hatipha.
57 Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
The children of Solomon’s servants: the children of Sotai, the children of Sophereth, the children of Perida,
58 da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
the children of Jaala, the children of Darkon, the children of Giddel,
59 Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
the children of Shephatiah, the children of Hattil, the children of Pochereth Hazzebaim, and the children of Amon.
60 Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
All the temple servants and the children of Solomon’s servants were three hundred ninety-two.
61 Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
These were those who went up from Tel Melah, Tel Harsha, Cherub, Addon, and Immer; but they could not show their fathers’ houses, nor their offspring, whether they were of Israel:
62 zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
The children of Delaiah, the children of Tobiah, the children of Nekoda: six hundred forty-two.
63 Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
Of the priests: the children of Hobaiah, the children of Hakkoz, the children of Barzillai, who took a wife of the daughters of Barzillai the Gileadite, and was called after their name.
64 Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
These searched for their genealogical records, but couldn’t find them. Therefore they were deemed disqualified and removed from the priesthood.
65 Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
The governor told them not to eat of the most holy things until a priest stood up to minister with Urim and Thummim.
66 Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
The whole assembly together was forty-two thousand three hundred sixty,
67 ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
in addition to their male servants and their female servants, of whom there were seven thousand three hundred thirty-seven. They had two hundred forty-five singing men and singing women.
68 Akwai dawakai 736, alfadarai 245
Their horses were seven hundred thirty-six; their mules, two hundred forty-five;
69 raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
their camels, four hundred thirty-five; their donkeys, six thousand seven hundred twenty.
70 Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
Some from among the heads of fathers’ households gave to the work. The governor gave to the treasury one thousand darics of gold, fifty basins, and five hundred thirty priests’ garments.
71 Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
Some of the heads of fathers’ households gave into the treasury of the work twenty thousand darics of gold, and two thousand two hundred minas of silver.
72 Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
That which the rest of the people gave was twenty thousand darics of gold, plus two thousand minas of silver, and sixty-seven priests’ garments.
73 Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,
So the priests, the Levites, the gatekeepers, the singers, some of the people, the temple servants, and all Israel lived in their cities. When the seventh month had come, the children of Israel were in their cities.

< Nehemiya 7 >