< Nehemiya 11 >

1 To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
The princes of the people lived in Jerusalem. The rest of the people also cast lots to bring one of ten to dwell in Jerusalem, the holy city, and nine parts in the other cities.
2 Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
The people blessed all the men who willingly offered themselves to dwell in Jerusalem.
3 Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
Now these are the chiefs of the province who lived in Jerusalem; but in the cities of Judah, everyone lived in his possession in their cities—Israel, the priests, the Levites, the temple servants, and the children of Solomon’s servants.
4 yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
Some of the children of Judah and of the children of Benjamin lived in Jerusalem. Of the children of Judah: Athaiah the son of Uzziah, the son of Zechariah, the son of Amariah, the son of Shephatiah, the son of Mahalalel, of the children of Perez;
5 da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
and Maaseiah the son of Baruch, the son of Colhozeh, the son of Hazaiah, the son of Adaiah, the son of Joiarib, the son of Zechariah, the son of the Shilonite.
6 Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
All the sons of Perez who lived in Jerusalem were four hundred sixty-eight valiant men.
7 Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
These are the sons of Benjamin: Sallu the son of Meshullam, the son of Joed, the son of Pedaiah, the son of Kolaiah, the son of Maaseiah, the son of Ithiel, the son of Jeshaiah.
8 da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
After him Gabbai and Sallai, nine hundred twenty-eight.
9 Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
Joel the son of Zichri was their overseer; and Judah the son of Hassenuah was second over the city.
10 Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
Of the priests: Jedaiah the son of Joiarib, Jachin,
11 da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
Seraiah the son of Hilkiah, the son of Meshullam, the son of Zadok, the son of Meraioth, the son of Ahitub, the ruler of God’s house,
12 tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
and their brothers who did the work of the house, eight hundred twenty-two; and Adaiah the son of Jeroham, the son of Pelaliah, the son of Amzi, the son of Zechariah, the son of Pashhur, the son of Malchijah,
13 da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
and his brothers, chiefs of fathers’ households, two hundred forty-two; and Amashsai the son of Azarel, the son of Ahzai, the son of Meshillemoth, the son of Immer,
14 da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
and their brothers, mighty men of valor, one hundred twenty-eight; and their overseer was Zabdiel, the son of Haggedolim.
15 Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
Of the Levites: Shemaiah the son of Hasshub, the son of Azrikam, the son of Hashabiah, the son of Bunni;
16 da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
and Shabbethai and Jozabad, of the chiefs of the Levites, who had the oversight of the outward business of God’s house;
17 Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
and Mattaniah the son of Mica, the son of Zabdi, the son of Asaph, who was the chief to begin the thanksgiving in prayer, and Bakbukiah, the second among his brothers; and Abda the son of Shammua, the son of Galal, the son of Jeduthun.
18 Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
All the Levites in the holy city were two hundred eighty-four.
19 Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
Moreover the gatekeepers, Akkub, Talmon, and their brothers, who kept watch at the gates, were one hundred seventy-two.
20 Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
The residue of Israel, of the priests, and the Levites were in all the cities of Judah, everyone in his inheritance.
21 Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
But the temple servants lived in Ophel; and Ziha and Gishpa were over the temple servants.
22 Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
The overseer also of the Levites at Jerusalem was Uzzi the son of Bani, the son of Hashabiah, the son of Mattaniah, the son of Mica, of the sons of Asaph, the singers responsible for the service of God’s house.
23 Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
For there was a commandment from the king concerning them, and a settled provision for the singers, as every day required.
24 Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
Pethahiah the son of Meshezabel, of the children of Zerah the son of Judah, was at the king’s hand in all matters concerning the people.
25 Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
As for the villages with their fields, some of the children of Judah lived in Kiriath Arba and its towns, in Dibon and its towns, in Jekabzeel and its villages,
26 Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
in Jeshua, in Moladah, Beth Pelet,
27 da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
in Hazar Shual, in Beersheba and its towns,
28 Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
in Ziklag, in Meconah and in its towns,
29 Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
in En Rimmon, in Zorah, in Jarmuth,
30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
Zanoah, Adullam, and their villages, Lachish and its fields, and Azekah and its towns. So they encamped from Beersheba to the valley of Hinnom.
31 Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
The children of Benjamin also lived from Geba onward, at Michmash and Aija, and at Bethel and its towns,
32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,
at Anathoth, Nob, Ananiah,
33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,
Hazor, Ramah, Gittaim,
34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
Hadid, Zeboim, Neballat,
35 da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
Lod, and Ono, the valley of craftsmen.
36 Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.
Of the Levites, certain divisions in Judah settled in Benjamin’s territory.

< Nehemiya 11 >