< Nehemiya 10 >

1 Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
Now those who sealed were: Nehemiah the governor, the son of Hacaliah, and Zedekiah,
2 da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
Seraiah, Azariah, Jeremiah,
3 da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
Pashhur, Amariah, Malchijah,
4 da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
Hattush, Shebaniah, Malluch,
5 da Harim, da Meremot, da Obadiya,
Harim, Meremoth, Obadiah,
6 da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
Daniel, Ginnethon, Baruch,
7 da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
Meshullam, Abijah, Mijamin,
8 da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
Maaziah, Bilgai, and Shemaiah. These were the priests.
9 Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
The Levites: Jeshua the son of Azaniah, Binnui of the sons of Henadad, Kadmiel;
10 ’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
and their brothers, Shebaniah, Hodiah, Kelita, Pelaiah, Hanan,
11 da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
Mica, Rehob, Hashabiah,
12 da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
Zaccur, Sherebiah, Shebaniah,
13 da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
Hodiah, Bani, and Beninu.
14 Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
The chiefs of the people: Parosh, Pahathmoab, Elam, Zattu, Bani,
15 da Bunni, da Azgad, da Bebai,
Bunni, Azgad, Bebai,
16 da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
Adonijah, Bigvai, Adin,
17 da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
Ater, Hezekiah, Azzur,
18 da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
Hodiah, Hashum, Bezai,
19 da Harif, da Anatot, da Nebai,
Hariph, Anathoth, Nobai,
20 da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
Magpiash, Meshullam, Hezir,
21 da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
Meshezabel, Zadok, Jaddua,
22 da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
Pelatiah, Hanan, Anaiah,
23 da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
Hoshea, Hananiah, Hasshub,
24 da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
Hallohesh, Pilha, Shobek,
25 da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
Rehum, Hashabnah, Maaseiah,
26 da Ahiya, da Hanan, da Anan,
Ahiah, Hanan, Anan,
27 da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
Malluch, Harim, and Baanah.
28 “Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
The rest of the people, the priests, the Levites, the gatekeepers, the singers, the temple servants, and all those who had separated themselves from the peoples of the lands to the law of God, their wives, their sons, and their daughters—everyone who had knowledge and understanding—
29 dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
joined with their brothers, their nobles, and entered into a curse and into an oath, to walk in God’s law, which was given by Moses the servant of God, and to observe and do all the commandments of Yahweh our Lord, and his ordinances and his statutes;
30 “Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
and that we would not give our daughters to the peoples of the land, nor take their daughters for our sons;
31 “Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
and if the peoples of the land bring wares or any grain on the Sabbath day to sell, that we would not buy from them on the Sabbath, or on a holy day; and that we would forego the seventh year crops and the exaction of every debt.
32 “Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
Also we made ordinances for ourselves, to charge ourselves yearly with the third part of a shekel for the service of the house of our God:
33 Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
for the show bread, for the continual meal offering, for the continual burnt offering, for the Sabbaths, for the new moons, for the set feasts, for the holy things, for the sin offerings to make atonement for Israel, and for all the work of the house of our God.
34 “Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
We, the priests, the Levites, and the people, cast lots for the wood offering, to bring it into the house of our God, according to our fathers’ houses, at times appointed year by year, to burn on Yahweh our God’s altar, as it is written in the law;
35 “Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
and to bring the first fruits of our ground and the first fruits of all fruit of all kinds of trees, year by year, to Yahweh’s house;
36 “Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
also the firstborn of our sons and of our livestock, as it is written in the law, and the firstborn of our herds and of our flocks, to bring to the house of our God, to the priests who minister in the house of our God;
37 “Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
and that we should bring the first fruits of our dough, our wave offerings, the fruit of all kinds of trees, and the new wine and the oil, to the priests, to the rooms of the house of our God; and the tithes of our ground to the Levites; for they, the Levites, take the tithes in all our farming villages.
38 Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
The priest, the descendent of Aaron, shall be with the Levites when the Levites take tithes. The Levites shall bring up the tithe of the tithes to the house of our God, to the rooms, into the treasure house.
39 Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”
For the children of Israel and the children of Levi shall bring the wave offering of the grain, of the new wine, and of the oil, to the rooms where the vessels of the sanctuary are, and the priests who minister, with the gatekeepers and the singers. We will not forsake the house of our God.

< Nehemiya 10 >