< Nahum 1 >

1 Jawabi game da Ninebe a littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.
The declaration about Nineveh. The book of the vision of Nahum, the Elkoshite.
2 Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya kuma. Ubangiji Allah mai kishi ne, mai ɗaukar fansa kuma. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa, yakan ci gaba da fushi a kan abokan gābansa.
Yahweh is a jealous God and avenges; Yahweh avenges and is full of wrath; Yahweh takes vengeance on his adversaries, and he continues his anger for his enemies.
3 Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai iko duka kuma. Ubangiji ba zai bar masu zunubi babu horo ba. Hanyarsa tana cikin guguwa da kuma hadari, gizagizai kuwa su ne ƙurar ƙafafunsa.
Yahweh is slow to anger and great in power; he will not allow the wicked to go unpunished. Yahweh makes his way in the whirlwind and the storm, and the clouds are the dust of his feet.
4 Yakan tsawata wa teku yă kuma busar da shi; yakan sa dukan koguna su kafe. Bashan da Karmel sun yi yaushi tohon Lebanon kuma ya koɗe.
He rebukes the sea and makes it dry; he dries up all the rivers. Bashan is weak, and Carmel also; the flowers of Lebanon are weak.
5 Duwatsu suna rawan jiki a gabansa tuddai kuma sun narke. Duniya da dukan abin da yake cikinta suna rawan jiki a gabansa.
The mountains shake in his presence, and the hills melt; the earth collapses in his presence, indeed, the world and all people who live in it.
6 Wa zai iya tsaya wa fushinsa? Wa yake da ikon jimre wa zafin hasalarsa? Ana zuba fushinsa kamar wuta; aka kuma ragargaza duwatsu a gabansa.
Who can stand before his wrath? Who can resist the fierceness of his anger? His wrath is poured out like fire, and the rocks are broken apart by him.
7 Ubangiji nagari ne, mafaka kuma a lokacin wahala. Yana kula da waɗanda suka dogara gare shi,
Yahweh is good, a stronghold in the day of trouble; and he is faithful to those who take refuge in him.
8 amma da ambaliyar ruwa zai kawo Ninebe ga ƙarshe; zai fafari maƙiyansa zuwa cikin duhu.
But he will make a full end to his enemies with an overwhelming flood; he will pursue them into darkness.
9 Dukan abin da suke ƙullawa game da Ubangiji zai kawo ga ƙarshe; wahala ba za tă sāke komowa ƙaro na biyu ba.
What are you people plotting against Yahweh? He will make a full end to it; trouble will not rise up a second time.
10 Za su sarƙafe a ƙaya, za su kuma bugu da ruwan inabinsu; za a laƙume su kamar busasshiyar ciyawa.
For they will become tangled up like thornbushes; they will be saturated in their own drink; they will be completely devoured by fire like dry stubble.
11 Daga cikinki, ya Ninebe wani ya fito wanda ya ƙulla wa Ubangiji makirci yana ba da mugayen shawarwari.
Someone arose among you, Nineveh, who planned evil against Yahweh, someone who promoted wickedness.
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Ko da yake sun yi tarayya, suna kuma da yawa, za a yanke su, a kawar a su. Ko da yake na ba ki azaba, ya Yahuda, ba zan ƙara ba ki azaba ba.
This is what Yahweh says, “Even if they are at their full strength and full numbers, they will nevertheless be sheared; their people will be no more. But you, Judah: Though I have afflicted you, I will afflict you no more.
13 Yanzu zan karya karkiyarsu daga wuyanki in kuma tsittsinke sarƙar da suka ɗaura ki.”
Now will I break that people's yoke from off you; I will break your chains.”
14 Ubangiji ya ba da umarni game da ke Ninebe, “Ba za ki sami zuriyar da za tă ci gaba da sunanki ba. Zan rurrushe siffofin da kuka sassaƙa da kuma gumakan da kuka ƙera gumakan da suke a cikin haikalin allolinku. Zan shirya kabarinki, domin ke muguwa ce.”
Yahweh has given a command about you, Nineveh: “There will be no more descendants bearing your name. I will cut off the carved figures and the cast metal figures from the houses of your gods. I will dig your graves, for you are contemptible.”
15 Duba, can a bisa duwatsu, ga ƙafafu mai kawo labari mai daɗi, wanda yake shelar salama! Ki yi bukukkuwanki, ya Yahuda, ki kuma cika wa’adodinki. Mugaye ba za su ƙara mamaye ki ba; domin za a hallaka su ƙaƙaf.
Look, on the mountains there are the feet of someone who is bringing good news, who is announcing peace! Celebrate your festivals, Judah, and keep your vows, for the wicked one will invade you no more; he is completely cut off.

< Nahum 1 >