< Mika 4 >

1 A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
Men det skal skje i de siste dager, da skal fjellet der Herrens hus står, være grunnfestet på toppen av fjellene, og høit hevet skal det være over alle høider; og folkeslag skal strømme op på det.
2 Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
Og mange hedningefolk skal gå avsted og si: Kom, la oss gå op til Herrens berg og til Jakobs Guds hus, så han kan lære oss sine veier, og vi ferdes på hans stier! For fra Sion skal lov utgå, og Herrens ord fra Jerusalem.
3 Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
Og han skal dømme mellem mange folkeslag og skifte rett for veldige hedningefolk helt til de fjerneste land, og de skal smi sine sverd om til hakker og sine spyd til vingårdskniver; folkene skal ikke lenger løfte sverd mot hverandre og ikke mere lære å føre krig,
4 Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
men de skal sitte hver under sitt vintre og sitt fikentre, og ingen skal skremme dem; for Herrens, hærskarenes Guds munn har talt.
5 Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
For alle folkene vandrer hvert i sin guds navn; men vi vandrer i Herrens, vår Guds navn evindelig og alltid.
6 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
På den dag, sier Herren, vil jeg samle de haltende og sanke sammen de bortdrevne og dem jeg har faret ille med,
7 Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
og jeg vil la de haltende bli i live som en rest og gjøre de langt bortdrevne til et tallrikt folk. Og Herren skal være konge over dem på Sions berg fra nu og til evig tid.
8 Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
Og du hjordens tårn, du Sions datters haug! Til dig skal det nå, ja, det skal komme det forrige herredømme, kongedømmet over Jerusalems datter.
9 Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
Hvorfor skriker du nu så høit? Er det da ingen konge i dig, eller er din rådgiver omkommet, siden veer har grepet dig som den fødende kvinnes?
10 Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
Vri dig og jamre dig, Sions datter, som en fødende kvinne! For nu må du dra ut av byen og bo ute på marken, og du skal komme like til Babel. Der skal du bli utfridd, der skal Herren løse dig ut av dine fienders hånd.
11 Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
Nu har mange folkeslag samlet sig mot dig, og de sier: Måtte det bli vanhelliget, så våre øine kan se med lyst på Sion!
12 Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
Men de kjenner ikke Herrens tanker og forstår ikke hans råd, at han har samlet dem som kornbånd til treskeplassen.
13 “Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.
Stå op og tresk, du Sions datter! For ditt horn vil jeg gjøre til jern, og dine klover vil jeg gjøre til kobber, og du skal knuse mange folk, og jeg vil lyse deres rov i bann til Herren og deres gods til all jordens herre.

< Mika 4 >