< Mika 4 >

1 A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
But in the latter days, it will happen that the mountain of Yahweh’s temple will be established on the top of the mountains, and it will be exalted above the hills; and peoples will stream to it.
2 Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
Many nations will go and say, “Come! Let’s go up to the mountain of Yahweh, and to the house of the God of Jacob; and he will teach us of his ways, and we will walk in his paths.” For the law will go out of Zion, and Yahweh’s word from Jerusalem;
3 Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
and he will judge between many peoples, and will decide concerning strong nations afar off. They will beat their swords into plowshares, and their spears into pruning hooks. Nation will not lift up sword against nation, neither will they learn war any more.
4 Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
But every man will sit under his vine and under his fig tree. No one will make them afraid, for the mouth of Yahweh of Armies has spoken.
5 Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
Indeed all the nations may walk in the name of their gods, but we will walk in the name of Yahweh our God forever and ever.
6 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
“In that day,” says Yahweh, “I will assemble that which is lame, and I will gather that which is driven away, and that which I have afflicted;
7 Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
and I will make that which was lame a remnant, and that which was cast far off a strong nation: and Yahweh will reign over them on Mount Zion from then on, even forever.”
8 Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
You, tower of the flock, the hill of the daughter of Zion, to you it will come. Yes, the former dominion will come, the kingdom of the daughter of Jerusalem.
9 Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
Now why do you cry out aloud? Is there no king in you? Has your counselor perished, that pains have taken hold of you as of a woman in travail?
10 Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
Be in pain, and labor to give birth, daughter of Zion, like a woman in travail; for now you will go out of the city, and will dwell in the field, and will come even to Babylon. There you will be rescued. There Yahweh will redeem you from the hand of your enemies.
11 Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
Now many nations have assembled against you, that say, “Let her be defiled, and let our eye gloat over Zion.”
12 Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
But they don’t know the thoughts of Yahweh, neither do they understand his counsel; for he has gathered them like the sheaves to the threshing floor.
13 “Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.
Arise and thresh, daughter of Zion, for I will make your horn iron, and I will make your hoofs bronze. You will beat in pieces many peoples. I will devote their gain to Yahweh, and their substance to the Lord of the whole earth.

< Mika 4 >