< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
Isus iziđe iz Hrama. Putom mu pristupiše učenici pokazujući mu hramsko zdanje.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
A on im reče: “Ne vidite li sve ovo? Zaista, kažem vam, ne, neće se ovdje ostaviti ni kamen na kamenu nerazvaljen.”
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
Dok je zatim na Maslinskoj gori sjedio, pristupiše k njemu učenici nasamo govoreći: “Reci nam kada će to biti i koji će biti znak tvojega Dolaska i svršetka svijeta?” (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
Isus im odgovori: “Pazite da vas tko ne zavede!
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
Mnogi će doista doći u moje ime i govoriti: 'Ja sam Krist!' I mnoge će zavesti.”
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
“A čut ćete za ratove i za glasove o ratovima. Pazite, ne uznemirujte se. Doista treba da se to dogodi, ali to još nije svršetak.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
Narod će ustati protiv naroda i kraljevstvo protiv kraljevstva; bit će gladi i potresa po raznim mjestima.
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
Ali sve je to samo početak trudova.”
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
“Tada će vas predavati na muke i ubijati vas. I svi će vas narodi zamrziti zbog imena moga.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
Mnogi će se tada sablazniti, izdavat će jedni druge i mrziti se među sobom.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
Ustat će mnogi lažni proroci i mnoge zavesti.
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
Razmahat će se bezakonje i ohladnjeti ljubav mnogih.
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
Ali tko ustraje do svršetka, bit će spašen.”
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
“I propovijedat će se ovo evanđelje Kraljevstva po svem svijetu za svjedočanstvo svim narodima. Tada će doći svršetak.”
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
“Kada dakle vidite da grozota pustoši, po proroštvu Daniela proroka, stoluje na svetome mjestu - tko čita, neka razumije:
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
koji se tada zateknu u Judeji, neka bježe u gore;
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
tko bude na krovu, neka ne silazi uzeti što iz kuće;
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
i tko bude u polju, neka se ne okreće natrag da uzme haljinu!”
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
“A jao trudnicama i dojiljama u one dane!”
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
“I molite da bijeg vaš ne bude zimi ili subotom
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
jer tada će biti velika tjeskoba kakve ne bijaše od početka svijeta sve do sada, a neće je ni biti.”
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
“I kad se ne bi skratili dani oni, nitko se ne bi spasio. No poradi izabranih skratit će se dani oni.”
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
“Ako vam tada tko rekne: 'Gle, evo Krista!' ili: 'Eno ga!' - ne povjerujte!
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Ustat će, doista, lažni kristi i lažni proroci i iznijeti znamenja velika i čudesa da, bude li moguće, zavedu i izabrane.”
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
“Eto, prorekao sam vam.”
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
“Reknu li vam dakle: 'Evo, u pustinji je!', ne izlazite; 'Evo ga u ložnicama!', ne vjerujte.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
Jer kao što munja izlazi od istoka i bljesne do zapada, tako će biti i s dolaskom Sina Čovječjega.”
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
“Gdje bude strvine, ondje će se skupljati orlovi.”
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
“A odmah nakon nevolje onih dana sunce će pomrčati i mjesec neće više svijetljeti i zvijezde će s neba padati i sile će se nebeske poljuljati.”
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
“I tada će se pojaviti znak Sina Čovječjega na nebu. I tada će proplakati sva plemena zemlje. I ugledat će Sina Čovječjega gdje dolazi na oblacima nebeskim s velikom moći i slavom.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
I razaslat će anđele svoje s trubljom velikom i sabrat će mu izabranike s četiri vjetra, s jednoga kraja neba do drugoga.”
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
“A od smokve se naučite prispodobi! Kad joj grana već omekša i lišće potjera, znate: blizu je ljeto.
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
Tako i vi kad sve to ugledate, znajte: blizu je, na vratima!”
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
“Zaista, kažem vam, ne, neće uminuti naraštaj ovaj dok se sve to ne zbude.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Nebo će i zemlja uminuti, ali riječi moje ne, neće uminuti.”
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
“A o onom danu i času nitko ne zna, pa ni anđeli nebeski, ni Sin, nego samo Otac.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Kao u dane Noine, tako će biti i Dolazak Sina Čovječjega.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
Kao što su u dane one - prije potopa - jeli i pili, ženili se i udavali do dana kad Noa uđe u korablju
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
i ništa nisu ni slutili dok ne dođe potop i sve odnije - tako će biti i Dolazak Sina Čovječjega.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Dvojica će tada biti u polju: jedan će se uzeti, drugi ostaviti.
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Dvije će mljeti u mlinu: jedna će se uzeti, druga ostaviti.”
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
“Bdijte dakle jer ne znate u koji dan Gospodin vaš dolazi.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
A ovo znajte: kad bi domaćin znao o kojoj straži kradljivac dolazi, bdio bi i ne bi dopustio potkopati kuće.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
Zato i vi budite pripravni jer u čas kad i ne mislite Sin Čovječji dolazi.”
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
“Tko li je onaj vjerni i razumni sluga što ga gospodar postavi nad svojim ukućanima da im izda hranu u pravo vrijeme?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Blago onome sluzi kojega gospodar kada dođe nađe da tako radi!
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
Zaista, kažem vam, postavit će ga nad svim imanjem svojim.”
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
“No rekne li taj zli sluga u srcu: 'Okasnit će gospodar moj'
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
pa stane tući sudrugove, jesti i piti s pijanicama,
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
doći će gospodar toga sluge u dan u koji mu se ne nada i u čas u koji i ne sluti;
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
rasjeći će ga i dodijeliti mu udes među licemjerima. Ondje će biti plač i škrgut zubi.”

< Mattiyu 24 >