< Markus 1 >

1 Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
Commencement de l'Évangile de Jésus-Christ, Fils de Dieu.
2 An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
Conformément à ce qui avait été écrit dans les prophètes: Voici, j'envoie mon messager devant ta face, qui préparera le chemin devant toi:
3 “muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
Voix de celui qui crie dans le désert: Préparez le chemin du Seigneur; aplanissez ses sentiers.
4 Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
Jean baptisait dans le désert, et prêchait le baptême de repentance, pour la rémission des péchés.
5 Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
Et toute la Judée et les habitants de Jérusalem allaient à lui, et ils étaient tous baptisés par lui dans le fleuve du Jourdain, en confessant leurs péchés.
6 Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
Jean était vêtu de poils de chameau, il avait une ceinture de cuir autour de ses reins, et il se nourrissait de sauterelles et de miel sauvage.
7 Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
Et il prêchait en disant: Il en vient un après moi, qui est plus puissant que moi, et dont je ne suis pas digne, en me baissant, de délier la courroie des souliers.
8 Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
Pour moi je vous ai baptisés d'eau, mais lui vous baptisera du Saint-Esprit.
9 A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
Il arriva, en ce temps-là, que Jésus vint de Nazareth de Galilée, et il fut baptisé par Jean dans le Jourdain.
10 Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
Et aussitôt, comme il sortait de l'eau, il vit les cieux s'ouvrir et le Saint-Esprit descendre sur lui comme une colombe.
11 Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
Et une voix vint des cieux, qui dit: Tu es mon Fils bien-aimé, en qui j'ai pris plaisir.
12 Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
Et aussitôt l'Esprit poussa Jésus au désert.
13 ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
Et il fut là au désert quarante jours, étant tenté par Satan; et il était avec les bêtes sauvages, et les anges le servaient.
14 Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
Or, après que Jean eut été mis en prison, Jésus s'en alla en Galilée, prêchant l'évangile du royaume de Dieu, et disant:
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
Le temps est accompli, et le royaume de Dieu approche. Repentez-vous et croyez à l'Évangile.
16 Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
Or, comme il marchait le long de la mer de Galilée, il vit Simon et André son frère, qui jetaient leurs filets dans la mer; car ils étaient pêcheurs.
17 Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
Alors Jésus leur dit: Suivez-moi, et je vous ferai pêcheurs d'hommes.
18 Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
Et aussitôt, laissant leurs filets, ils le suivirent.
19 Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
Et de là passant un peu plus avant, il vit dans une barque Jacques, fils de Zébédée, et Jean son frère, qui raccommodaient leurs filets.
20 Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
Au même instant il les appela; et eux, laissant Zébédée leur père dans la barque avec les ouvriers, le suivirent.
21 Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
Ensuite ils entrèrent à Capernaüm; et Jésus, étant d'abord entré dans la synagogue le jour du sabbat, y enseignait.
22 Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
Et ils étaient étonnés de sa doctrine; car il les enseignait comme ayant autorité, et non pas comme les scribes.
23 Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
Or, il se trouva dans leur synagogue un homme possédé d'un esprit immonde, qui s'écria, et dit:
24 “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
Ah! qu'y a-t-il entre toi et nous, Jésus Nazarien? Es-tu venu pour nous perdre? Je sais qui tu es; le Saint de Dieu.
25 Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
Mais Jésus le tança en disant: Tais-toi, et sors de lui.
26 Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
Alors l'esprit immonde l'agitant avec violence et jetant un grand cri, sortit de lui.
27 Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
Et ils furent tous étonnés, de sorte qu'ils se demandaient entre eux: Qu'est-ce que ceci? Quelle est cette nouvelle doctrine? Car il commande avec autorité même aux esprits immondes, et ils lui obéissent.
28 Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
Et sa réputation se répandit aussitôt par toute la contrée des environs de la Galilée.
29 Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
Aussitôt après, étant sortis de la synagogue, ils vinrent avec Jacques et Jean dans la maison de Simon et d'André.
30 Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
Or, la belle-mère de Simon était au lit, malade de la fièvre; et aussitôt ils lui parlèrent d'elle.
31 Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
Alors s'approchant, il la fit lever en la prenant par la main; et au même instant la fièvre la quitta, et elle les servit.
32 A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
Sur le soir, quand le soleil fut couché, ils lui amenèrent tous les malades, et les démoniaques.
33 Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
Et toute la ville était assemblée à la porte de la maison.
34 Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
Et il guérit plusieurs malades de diverses maladies, et il chassa plusieurs démons, ne leur permettant pas de dire qu'ils le connaissaient.
35 Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
Le matin, comme il faisait encore fort obscur, s'étant levé, il sortit et s'en alla dans un lieu écarté; et il y priait.
36 Siman da abokansa suka fita nemansa.
Et Simon, et ceux qui étaient avec lui allèrent à sa recherche.
37 Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
Et l'ayant trouvé, ils lui dirent: Tous te cherchent.
38 Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
Et il leur dit: Allons dans les bourgades voisines, afin que j'y prêche aussi; car c'est pour cela que je suis venu.
39 Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
Et il prêchait dans leurs synagogues, par toute la Galilée, et il chassait les démons.
40 Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
Et un lépreux vint à lui, se jeta à genoux, le pria et lui dit: Si tu veux, tu peux me nettoyer.
41 Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
Et Jésus, ému de compassion, étendit la main, le toucha, et lui dit: Je le veux, sois nettoyé.
42 Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
Et dès qu'il eut dit cela, la lèpre quitta aussitôt cet homme, et il fut nettoyé.
43 Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
Et Jésus le renvoya aussitôt avec de sévères recommandations, et lui dit:
44 “Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
Garde-toi d'en rien dire à personne; mais va-t'en et montre-toi au sacrificateur, et offre pour ta purification ce que Moïse a commandé, afin que cela leur serve de témoignage.
45 A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.
Mais cet homme étant sorti, se mit à publier hautement la chose et à la divulguer, en sorte que Jésus ne pouvait plus entrer ouvertement dans la ville; mais il se tenait dehors dans des lieux écartés, et de toutes parts on venait à lui.

< Markus 1 >