< Markus 1 >

1 Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
Commencement de l'Évangile de Jésus-Christ, Fils de Dieu.
2 An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
Selon ce qui est écrit dans le prophète Isaïe: " Voilà que j'envoie mon messager devant vous, pour vous frayer le chemin.
3 “muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
Une voix crie dans le désert: Préparez le chemin du Seigneur, aplanissez ses sentiers. "
4 Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
Jean parut, baptisant dans le désert, et prêchant le baptême de pénitence pour la rémission des péchés.
5 Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
Tout le pays de Judée et tous les habitants de Jérusalem venaient à lui, et, confessant leurs péchés, ils recevaient de lui le baptême dans le fleuve du Jourdain.
6 Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
Or, Jean était vêtu de poils de chameau; il avait autour de ses reins une ceinture de cuir, et se nourrissait de sauterelles et de miel sauvage. Et il prêchait ainsi:
7 Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
" Il vient après moi, celui qui est plus puissant que moi, et je ne suis pas digne de délier, en me baissant, les cordons de sa chaussure.
8 Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
Moi, je vous ai baptisés dans l'eau, mais lui vous baptisera dans le Saint-Esprit. "
9 A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
Or, il arriva en ces jours-là que Jésus vint de Nazareth, ville de Galilée, et il fut baptisé par Jean dans le Jourdain.
10 Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
Et, comme il sortait de l'eau, il vit les cieux s'ouvrir et l'Esprit-Saint descendre sur lui comme une colombe.
11 Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
Et du ciel une voix se fit entendre: " Tu es mon Fils bien-aimé, en toi j'ai mis mes complaisances. "
12 Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
Et aussitôt L'Esprit poussa Jésus au désert.
13 ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
Et il y demeura quarante jours, tenté par Satan; il était parmi les bêtes sauvages, et les anges le servaient.
14 Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
Après que Jean eut été mis en prison, Jésus vint en Galilée, prêchant l'Évangile du royaume de Dieu.
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
Il disait: " Le temps est accompli, et le royaume de Dieu est proche; repentez-vous et croyez à l'Évangile. "
16 Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
Passant le long de la mer de Galilée, il vit Simon et André son frère qui jetaient leurs filets dans la mer, car ils étaient pêcheurs.
17 Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
Jésus leur dit: " Venez à ma suite, et je vous ferai devenir pêcheurs d'hommes. "
18 Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
Aussitôt, laissant leurs filets, ils le suivirent.
19 Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
Un peu plus loin, il vit Jacques, fils de Zébédée, et Jean son frère, qui étaient, eux aussi, dans une barque, réparant leurs filets.
20 Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
Il les appela aussitôt; et, laissant leur père Zébédée dans la barque avec les mercenaires, ils le suivirent.
21 Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
Ils se rendirent à Capharnaüm, et dès le premier sabbat, Jésus entrant dans la synagogue, se mit à enseigner.
22 Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
Et ils étaient frappés de sa doctrine, car il les enseignait comme ayant autorité, et non comme les Scribes.
23 Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
Or il se trouva dans leur synagogue un homme possédé d'un esprit impur, qui s'écria:
24 “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
" Qu'avons-nous à faire avec vous, Jésus de Nazareth? Vous êtes venu pour nous perdre! Je sais qui vous êtes, le Saint de Dieu. "
25 Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
Mais Jésus, lui parlant avec menace: " Tais-toi, dit-il, et sors de cet homme. "
26 Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
Et l'esprit impur, l'agitant violemment, sortit de lui en jetant un grand cri.
27 Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
Tous furent saisis d'étonnement, de sorte qu'ils se demandaient entre eux: " Qu'est-ce que ceci? Quelle est cette doctrine nouvelle? Car il commande en maître, même aux esprits impurs, et ils lui obéissent. "
28 Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
Et sa renommée se répandit aussitôt dans tout le pays qui avoisine la Galilée.
29 Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
En sortant de la synagogue, ils allèrent aussitôt dans la maison de Simon et d'André, avec Jacques et Jean.
30 Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
Or, la belle-mère de Simon était au lit, ayant la fièvre; aussitôt ils parlèrent d'elle à Jésus.
31 Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
Il s'approcha et la fit lever, en la prenant par la main; au même instant la fièvre la quitta, et elle se mit à les servir.
32 A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
Sur le soir, après le coucher du soleil, il lui amenèrent tous les malades et les démoniaques,
33 Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
et toute la ville se pressait devant la porte.
34 Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
Il guérit beaucoup de malades affligés de diverses infirmités, et il chassa beaucoup de démons; mais il ne leur permettait pas de parler, parce qu'ils le connaissaient.
35 Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
Le lendemain, s'étant levé longtemps avant le jour, il sortit, alla dans un lieu solitaire, et il y pria.
36 Siman da abokansa suka fita nemansa.
Simon et ceux qui étaient avec lui se mirent à sa recherche;
37 Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
et l'ayant trouvé, ils lui dirent: " Tout le monde vous cherche. "
38 Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
Il leur répondit: " Allons ailleurs dans les bourgades voisines, afin que j'y prêche aussi; car c'est pour cela que je suis sorti. "
39 Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
Et il prêchait dans leurs synagogues, parcourant la Galilée entière, et chassait les démons.
40 Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
Un lépreux vint à lui, et se jetant à ses genoux, il lui dit d'un ton suppliant: " Si vous voulez, vous pouvez me guérir. "
41 Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
Emu de compassion, Jésus étendit la main, et le toucha, en disant: " Je le veux, sois guéri. "
42 Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
Et dès qu'il eut parlé, la lèpre quitta cet homme, et il fut guéri.
43 Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
Aussitôt Jésus le renvoya, en lui disant d'un ton sévère:
44 “Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
" Garde-toi d'en parler à personne; mais va te montrer au prêtre, et offre pour ta guérison ce que Moïse a ordonné pour l'attester au peuple. "
45 A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.
Mais cet homme étant parti, se mit à raconter et à publier partout ce qui s'était passé: de sorte que Jésus ne pouvait plus entrer publiquement dans une ville; il se tenait dehors, dans des lieux solitaires, et l'on venait à lui de tous côtés.

< Markus 1 >