< Markus 3 >

1 Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
Puis il entra encore dans la Synagogue, et il y avait là un homme qui avait une main sèche.
2 Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
Et ils l'observaient, pour voir s'il le guérirait le [jour du] Sabbat, afin de l'accuser.
3 Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
Et [Jésus] dit à l'homme qui avait la main sèche: lève-toi, et [te place] là au milieu.
4 Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
Puis il leur dit: est-il permis de faire du bien [les jours] de Sabbat, ou de faire du mal? de sauver une personne, ou de la tuer? mais ils se turent.
5 Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
Alors les regardant de tous côtés avec indignation, et étant tout ensemble affligé de l'endurcissement de leur cœur, il dit à cet homme: étends ta main; et il l'étendit; et sa main fut rendue saine comme l'autre.
6 Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
Alors les Pharisiens étant sortis, ils consultèrent contre lui avec les Hérodiens, comment ils feraient pour le perdre.
7 Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
Mais Jésus se retira avec ses Disciples vers la mer, et une grande multitude le suivit de Galilée, et de Judée, et de Jérusalem, et d'Idumée, et de delà le Jourdain.
8 Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
Et ceux des environs de Tyr et de Sidon, ayant entendu les grandes choses qu'il faisait, vinrent vers lui en grand nombre.
9 Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
Et il dit à ses Disciples, qu'une petite nacelle ne bougeât point de là pour le servir, à cause des troupes, afin qu'elles ne le pressassent point.
10 Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
Car il en avait guéri beaucoup, de sorte que tous ceux qui étaient affligés de quelque fléau, se jetaient sur lui, pour le toucher.
11 Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
Et les esprits immondes, quand ils le voyaient, se prosternaient devant lui, et s'écriaient, en disant: tu es le Fils de Dieu.
12 Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
Mais il leur défendait avec de grandes menaces de le faire connaître.
13 Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
Puis il monta sur une montagne, et appela ceux qu'il voulut, et ils vinrent à lui.
14 Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
Et il en ordonna douze pour être avec lui, et pour les envoyer prêcher;
15 don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
Et afin qu'ils eussent la puissance de guérir les maladies, et de chasser les démons hors [des possédés].
16 Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
[Et ce sont ici les noms de ces douze], Simon qu'il surnomma Pierre.
17 Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
Et Jacques fils de Zébédée, et Jean, frère de Jacques, auxquels il donna le nom de Boanergès, qui veut dire, fils de tonnerre.
18 Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
Et André, et Philippe, et Barthélemy, et Matthieu, et Thomas, et Jacques [fils] d'Alphée, et Thaddée, et Simon le Cananéen,
19 da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
Et Judas Iscariot, qui même le trahit.
20 Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
Puis ils vinrent en la maison, et il s'y assembla encore une si grande multitude, qu'ils ne pouvaient pas même prendre leur repas.
21 Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
Et quand ses parents eurent entendu cela, ils sortirent pour se saisir de lui; car ils disaient qu'il était hors du sens.
22 Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
Et les Scribes qui étaient descendus de Jérusalem, disaient: Il a Béelzébul, et il chasse les démons par le prince des démons.
23 Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
Mais [Jésus] les ayant appelés, leur dit par des similitudes: comment Satan peut-il chasser Satan dehors?
24 In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
Car si un Royaume est divisé contre soi-même, ce Royaume-là ne peut point subsister.
25 In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
Et si une maison est divisée contre elle-même, cette maison-là ne peut point subsister.
26 In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
Si donc Satan s'élève contre lui-même, et est divisé, il ne peut point se soutenir, mais il tend à sa fin.
27 Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
Nul ne peut entrer dans la maison d'un homme fort, et piller son bien, si auparavant il n'a lié l'homme fort; mais alors il pillera sa maison.
28 Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
En vérité je vous dis, que toutes sortes de péchés seront pardonnés aux enfants des hommes, et aussi [toutes sortes] de blasphèmes par lesquels ils auront blasphémé;
29 Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Mais quiconque aura blasphémé contre le Saint-Esprit, n'aura jamais de pardon, mais il sera soumis à une condamnation éternelle. (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
Or c'était parce qu'ils disaient: il est possédé d'un esprit immonde.
31 Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
Sur cela ses frères et sa mère arrivèrent là, et se tenant dehors ils l'envoyèrent appeler; et la multitude était assise autour de lui.
32 Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
Et on lui dit: voilà ta mère et tes frères là dehors, qui te demandent.
33 Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
Mais il leur répondit, en disant: qui est ma mère, et qui sont mes frères?
34 Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
Et après avoir regardé de tous côtés ceux qui étaient assis autour de lui, il dit: voici ma mère et mes frères.
35 Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”
Car quiconque fera la volonté de Dieu, celui-là est mon frère, et ma sœur, et ma mère.

< Markus 3 >