< Luka 9 >

1 Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
Then called he the. xii. to gether and gave them power and auctorite over all devyls and that they myght heale diseases.
2 Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
And he sent them to preache the kyngdome of God and to cure the sick.
3 Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
And he sayd to them: Take nothinge to sucker you by ye waye: nether staffe nor scripe nether breed nether money nether have twoo cootes.
4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
And whatsoever housse ye enter into there abyde and thence departe.
5 In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
And whosoever will not receave you when ye go out of that cite shake of the very dust from youre fete for a testimony agaynst them.
6 Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
And they went out and went thorow the tounes preachinge the gospell and healynge every wheare.
7 Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
And Herod the tetrarch herde of all that was done of him and douted because that it was sayde of some that Iohn was rysen agayne from deeth:
8 waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
and of some that Helyas had apered: and of other that one of the olde prophetes was rysen agayne.
9 Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
And Herod sayde: Iohn have I behedded: who then is this of whom I heare suche thinges? And he desyred to se him.
10 Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
And the Apostles retourned and tolde him what great thinges they had done. And he toke them and went a syde into a solitary place nye to a citie called Bethsaida.
11 Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
And ye people knewe of it and folowed him. And he receaved them and spake vnto them of the kyngdome of God and healed them that had nede to be healed.
12 Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
And when ye daye beganne to weare awaye then came the twelve and sayde vnto him: sende ye people awaye that they maye goo into the tounes and villages roundabout and lodge and get meate for we are here in a place of wyldernes.
13 Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
But he sayde vnto them: Geve ye the to eate. And they sayde. We have no moo but fyve loves and two fisshes except we shuld goo and bye meate for all this people.
14 Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
And they were about a fyve thousand men. And he sayde to his disciples: Cause them to syt doune by fyfties in a company.
15 Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
And they dyd soo and made them all syt doune.
16 Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
And he toke the fyve loves and the two fisshes and loked vp to heven and blessed them and brake and gave to the disciples to set before ye people.
17 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
And they ate and were all satisfied. And ther was taken vp of that remayned to the twelve baskettes full of broken meate.
18 Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
And it fortuned as he was alone prayinge his disciples were wt him and he axed the sayinge: Who saye ye people yt I am?
19 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
They answered and sayd: Iohn Baptist. Some saye Helyas. And some saye one of the olde prophetes is rysen agayne.
20 “Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
He sayde vnto the: Who saye ye that I am? Peter answered and sayde: thou arte the Christ of god.
21 Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
And he warned and commaunded them that they shuld tell no man yt thinge
22 Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
sayinge: that the sonne of man must suffre many thinges and be reproved of the elders and of the hye prestes and scribes and be slayne and the thirde daye ryse agayne.
23 Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
And he sayde to them all yf eny man will come after me let him denye him sylfe and take vp his crosse dayly and folowe me.
24 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
Whosoever will save his lyfe shall lose it. And who soever shall lose his lyfe for my sake the same shall save it.
25 Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
For what avauntageth it a man to wynne the whole worlde yf he loose him sylfe or runne in domage of him sylfe?
26 Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
For whosoever is ashamed of me and of my sayinges: of him shall the sonne of man be ashamed when he cometh in his awne glorie and in the glorie of his father and of the holy angels.
27 “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
And I tell you of a surety: There be some of the yt stonde here which shall not tast of deeth tyll they se ye kyngdome of god.
28 Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
And it folowed about an. viii. dayes after thoose sayinges that he toke Peter Iames and Iohn and went vp into a moutayne to praye.
29 Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
And as he prayed ye facion of his countenaunce was changed and his garment was whyte and shoone.
30 Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
And beholde two men talked wt him and they were Moses and Helyas
31 Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
which appered gloriously and spake of his departinge which he shuld ende at Ierusalem.
32 Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
Peter and they that were with him were hevy with slepe. And when they woke they sawe his glorie and two men stondinge with him.
33 Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
And it chaunsed as they departed fro him Peter sayde vnto Iesus: Master it is good beinge here for vs. Let vs make thre tabernacles one for the and one for Moses and one for Helyas: and wist not what he sayde.
34 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
Whyll he thus spake ther came a cloude and shadowed them: and they feared when they were come vnder the cloude.
35 Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
And ther came a voyce out of the cloude sayinge: This is my deare sonne heare him.
36 Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
And assone as ye voyce was past Iesus was founde alone. And they kept it cloose and tolde noo man in thoose dayes eny of those thinges which they had sene.
37 Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
And it chaunsed on the nexte daye as they came doune from the hyll moche people met him.
38 Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
And beholde a man of the copany cryed out sayinge: Master I beseche ye beholde my sonne for he is all that I have:
39 Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
and se a sprete taketh him and sodenly he cryeth and he teareth him that he fometh agayne and with moche payne departeth fro him when he hath rent him and
40 Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
I besought thy disciples to cast him out and they coulde not.
41 Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
Iesus answered and sayde: O generacion with oute fayth and croked: how longe shall I be with you? and shall suffre you? Bringe thy sonne hidder.
42 Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
As he yet was a cominge the fende ret him and tare him. And Iesus rebuked ye vnclene sprete and healed the childe and delivered him to his father.
43 Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
And they were all amased at ye mighty power of God. Whyll they wondred every one at all thinges which he dyd he sayd vnto his disciples:
44 “Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
Let these sayinges synke doune into youre eares. The tyme will come when the sonne of man shalbe delivered into the hondes of men.
45 Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
But they wist not what yt worde meant and yt was hyd fro the that they vnderstode yt not. And they feared to axe him of that sayinge.
46 Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
Then ther arose a disputacion amoge the: who shuld be the greatest.
47 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
When Iesus perceaved ye thoughtes of their hertes he toke a chylde and set him hard by him
48 Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
and sayd vnto the: Whosoever receaveth this chylde in my name receaveth me. And whosoever receaveth me receaveth him yt sent me. For he yt is least amonge you all the same shalbe greate.
49 Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
And Iohn answered and sayde: Master we sawe one castinge out devyls in thy name and we forbade him because he foloweth not with vs.
50 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
And Iesus sayde vnto him: forbyd ye him not. For he that is not agaynst vs is wt vs.
51 Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
And it folowed when the tyme was come yt he shulde be receaved vp then he set his face to goo to Hierusalem
52 Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
and sent messengers before him. And they went and entred into a citie of the Samaritans to make redy for him.
53 Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
But they wolde not receave him be cause his face was as though he wolde goo to Ierusalem.
54 Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
When his disciples Iames and Iohn sawe yt they sayde: Lorde wilt thou that we comaunde that fyre come doune from heven and consume them even as Helias dyd?
55 Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
Iesus turned about and rebuked them sayinge: ye wote not what maner sprete ye are of.
56 Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
The sonne of ma ys not come to destroye mennes lives but to save them. And they went to another toune.
57 Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
And it chaunsed as he went in the waye a certayne man sayd vnto him: I will folowe the whither soever thou goo.
58 Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
Iesus sayd vnto him: foxes have holes and bryddes of ye ayer have nestes: but the sonne of man hath not where on to laye his heed.
59 Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
And he sayde vnto another: folowe me. And the same sayde: Lorde suffre me fyrst to goo and bury my father.
60 Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
Iesus sayd vnto him: Let the deed bury their deed: but goo thou and preache the kyngdome of God.
61 Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
And another sayde: I wyll folowe the Lorde: but let me fyrst goo byd them fare well which are at home at my housse.
62 Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”
Iesus sayde vnto him: No man that putteth his honde to the plowe and loketh backe is apte to the kyngdome of God.

< Luka 9 >