< Luka 8 >

1 Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
Kwasekusithi emva kwalokho, yena wadabula imizi lemizana, ememezela lokutshumayela indaba ezinhle zombuso kaNkulunkulu; labalitshumi lambili babelaye,
2 da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
labesifazana abathile ababesiliswe kubomoya ababi lemikhuhlaneni, uMariya othiwa nguMagadalena, okwaphuma kuye amadimoni ayisikhombisa,
3 Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
loJowana umkaKuza induna kaHerodi, loSusana, labanye abanengi, ababemsiza ngempahla zabo.
4 Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
Kwathi sekubuthene ixuku elikhulu, njalo bevela emizini ngemizi besiza kuye, wakhuluma ngomfanekiso,
5 “Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
wathi: Umhlanyeli waphuma ukuyahlanyela inhlanyelo yakhe; kwathi ekuhlanyeleni kwakhe, enye yawela eceleni kwendlela; yasinyathelwa ngenyawo, lenyoni zezulu zayidla zayiqeda.
6 Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
Lenye yawela edwaleni, kwathi ekukhuleni yabuna, ngoba yaswela ubumanzi.
7 Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
Lenye yawela phakathi kwameva, ameva asemila layo ayiminyanisa.
8 Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Lenye yawela emhlabathini omuhle, yakhula yathela ikhulu. Esetshilo lezizinto wamemeza wathi: Olendlebe zokuzwa akezwe.
9 Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
Abafundi bakhe basebembuza besithi: Ungaba yini lumfanekiso?
10 Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
Wasesithi: Kuphiwe kini ukwazi imfihlo zombuso kaNkulunkulu; kodwa kwabanye ngemifanekiso, ukuze bebona bangaboni, njalo besizwa bangaqedisisi.
11 “Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
Lomfanekiso uyilokhu: Inhlanyelo iyilizwi likaNkulunkulu.
12 Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
Labaseceleni kwendlela yilabo abathi sebezwile, besekufika udiyabhola alisuse ilizwi enhliziyweni zabo, ukuze bangakholwa basindiswe.
13 Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
Labasedwaleni yilabo, abathi belizwile, balemukele ilizwi ngentokozo, kodwa laba kabalampande, abakholwa okwesikhathi, kuthi ngesikhathi sokulingwa bawe.
14 Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
Lewele phakathi kwameva, yilabo abathi sebezwile, bahambe baminyaniswe yikukhathalela lenotho lenkanuko yempilo, njalo bangatheli izithelo ezivuthiweyo.
15 Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
Kodwa esemhlabathini omuhle, yilabo abathi belizwile ilizwi balilondoloze enhliziyweni enhle lelungileyo, bathela izithelo ngokubekezela.
16 “Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
Njalo kakho othi eselumathise isibane, asembese ngesitsha, kumbe asibeke ngaphansi kombheda, kodwa usibeka esiqobaneni sesibane, ukuze abangenayo babone ukukhanya.
17 Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
Ngoba kakukho okufihliweyo, okungasoze kube sobala; lokuthukuziweyo, okungayikwaziwa lokungayikulethwa obala.
18 Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Ngakho qaphelisani ukuthi lizwa njani; ngoba loba ngubani olakho, uzaphiwa; kodwa loba ngubani ongelakho, uzakwemukwa lalokho acabanga ukuthi ulakho.
19 Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
Kwasekufika kuye unina labafowabo, kodwa abazange bamfinyelele ngenxa yexuku.
20 Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
Wasebikelwa ngabanye abathi: Unyoko labafowenu bemi phandle, bafuna ukukubona.
21 Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
Kodwa waphendula wathi kubo: Umama labafowethu yilabo, abalizwayo ilizwi likaNkulunkulu balenze.
22 Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
Kwasekusithi ngolunye lwezinsuku, wangena emkhunjini yena labafundi bakhe, wasesithi kubo: Asichaphele ngaphetsheya kwechibi; basuka-ke.
23 Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
Kwathi behamba ngomkhumbi, walala ubuthongo; isiphepho esikhulu somoya sasesisehlela phansi echibini, bagcwalelwa ngamanzi, babesengozini.
24 Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
Basebesondela bamvusa, besithi: Nkosi, nkosi, siyabhubha! Wasevuka wakhuza umoya lamagagasi amakhulu amanzi; kwasekusima, kwasekusiba lokuthula.
25 Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
Wasesithi kubo: Lungaphi ukholo lwenu? Basebesesaba bamangala, bakhulumisana besithi: Kambe ungubani lo, ukuthi alaye ngitsho imimoya lamanzi, njalo kumlalele?
26 Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
Basebesiya ngomkhumbi elizweni lamaGadarene, eliqondene leGalili.
27 Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
Kwathi esephumele emhlabathini, yamhlangabeza indoda ethile ivela emzini, eyayilamadimoni okwesikhathi eside, njalo ingembathi isembatho, ingahlali endlini, kodwa emangcwabeni.
28 Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
Yathi imbona uJesu, yamemeza, yawa phansi phambi kwakhe, yathi ngelizwi elikhulu: Ngilani lawe, Jesu, Ndodana kaNkulunkulu oPhezukonke? Ngiyakuncenga, ungangihluphi.
29 Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
Ngoba walaya umoya ongcolileyo ukuthi aphume kulowomuntu; ngoba wayesembambe okwezikhathi ezinengi, walindwa ebotshiwe ngamaketane lezibopho, kodwa eseqamule izibopho waqhutshelwa enkangala lidimoni.
30 Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
UJesu wasembuza, wathi: Ungubani ibizo lakho? Wasesithi: NguLegiyoni; ngoba amadimoni amanengi ayengene kuye.
31 Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
Asemncenga ukuthi angawalayi ukuya emgodini ongelamkhawulo. (Abyssos g12)
32 A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
Kwakukhona lapho umhlambi wengulube ezinengi usidla entabeni; asemncenga ukuthi awavumele angene kuzo. Wasewavumela.
33 Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
Kwathi amadimoni esephumile kulowomuntu angena engulubeni; umhlambi wasuphaphatheka usuka eliweni usiya echibini, waminzwa.
34 Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
Kwathi ababezelusile bebona okwenzakeleyo babaleka, basuka bayabika emzini, lemaphandleni.
35 Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
Basebephuma ukuyabona okwenzakeleyo; bafika kuJesu, bamfica umuntu okwakuphume kuye amadimoni ehlezi enyaweni zikaJesu, embethe esephelele engqondweni; basebesesaba.
36 Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
Basebebatshela lalabo ababebonile ukuthi usindiswe njani owayengenwe ngamadimoni.
37 Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
Ixuku lonke lesigaba samaGadarene esizingelezeleyo laselimcela ukuthi asuke kubo, ngoba babanjwa yikwesaba okukhulu; yena wasengena emkhunjini waphindela emuva.
38 Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
Kodwa indoda okwakuphume kuyo amadimoni yamncenga ukuthi ibe laye. Kodwa uJesu wayiyekela yahamba, esithi:
39 “Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
Buyela endlini yakho, ulandise ukuthi kungakanani uNkulunkulu akwenze kuwe. Wasesuka wahamba, etshumayela phakathi komuzi wonke ukuthi kungakanani uJesu ayekwenzile kuye.
40 Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
Kwasekusithi ekubuyeni kukaJesu, ixuku lamthakazelela; ngoba bonke babemlindele.
41 Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
Njalo khangela, kwafika indoda, uJayirosi ngebizo, yona ingumphathi wesinagoge, yasisiwa phansi enyaweni zikaJesu yamncenga ukuthi angene endlini yayo;
42 domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
ngoba yayilendodakazi eyodwa ezelweyo eyayingaba leminyaka elitshumi lambili, njalo yona yayisisifa. Kwathi esahamba amaxuku amcindezela.
43 A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
Lowesifazana owayelomopho wegazi okweminyaka elitshumi lambili, echithe konke okwempilo yakhe kubelaphi engelakusiliswa langubani,
44 Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
wasondela ngemva kwakhe, wathinta umphetho wesembatho sakhe; njalo wahle wakhawula umopho wegazi lakhe.
45 Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
UJesu wasesithi: Ngubani ongithintileyo? Kwathi lapho bephika bonke, uPetro wathi lababelaye: Nkosi, ixuku likuminyanisile likucindezele, kodwa uthi: Ngubani ongithintileyo?
46 Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
Kodwa uJesu wathi: Ukhona ongithintileyo; ngoba mina ngazile ukuthi amandla aphumile kimi.
47 Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
Kwathi owesifazana ebona ukuthi kafihlakalanga, weza ethuthumela, wawa phambi kwakhe, walandisa phambi kwabantu bonke ukuthi umthinte ngesizatho bani, lokuthi uhle wasila njani.
48 Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
Wasesithi kuye: Mana isibindi, ndodakazi, ukholo lwakho lukusindisile; hamba ngokuthula.
49 Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
Esakhuluma, kwafika umuntu evela endlini yomphathi wesinagoge, wathi kuye: Indodakazi yakho isifile; ungamhluphi uMfundisi.
50 Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
Kodwa uJesu esizwa, wamphendula, wathi: Ungesabi; kholwa kuphela, njalo izasindiswa.
51 Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
Futhi esengenile endlini, kavumanga ukuthi kungene muntu, ngaphandle kukaPetro loJakobe loJohane, loyise wendodakazi lonina.
52 Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
Njalo bakhala bonke, beyililela. Kodwa wathi: Lingakhali; kayifanga, kodwa ilele.
53 Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
Basebemhleka usulu, besazi ukuthi ifile.
54 Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
Kodwa yena esebakhuphele phandle bonke, wabamba isandla sayo, wamemeza, esithi: Ndodakazi, vuka!
55 Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
Wasubuya umoya wayo, yasivuka khona lapho; waselaya ukuthi kayiphiwe ukudla.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.
Abazali bayo basebemangala kakhulu; kodwa wabalaya ukuthi bangatsheli muntu okwenzakeleyo.

< Luka 8 >