< Luka 8 >

1 Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
EIA kekahi, ma ia hope iho kaa hele ae la oia i na kulanakauhale a me na kauhale a pau, e hai ana a e hoike ana i ka olelo maikai no ke aupuni o ke Akua; me ia pu no hoi ka poe umikumamalua;
2 da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
A me kekahi mau wahine i hoolaia i na uhane ino a me na nawaliwali, o Maria i kapaia o Magedalena, noloko mai ona i puka mai ai na daimonio ehiku;
3 Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
A me Ioana ka wahine a Kuza a ka puuku o Herode, a me Susana, a me na mea e ae he nui, o ka poe i malama ia ia me kauwahi o ko lakou waiwai.
4 Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
A akoakoa mai la na kanaka he nui wale, o na mea hoi i hele mai io na la, mai loko mai o na kulanakauhale, olelo mai oia ma ka olelonane;
5 “Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
Hele aku la ka mea lulu hua e lulu iho i kana hua; a i kona lulu ana, helelei kekahi ma kapa alanui; a hehiia iho la, a ua aiia iho la e na manu o ka lewa.
6 Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
A helelei iho la kekahi maluna o ka pohaku; a kupu ae la, mae koke iho la ia, no ka mea, aohe ona mau.
7 Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
A helelei iho la kekahi iwaena o ke kakalaioa; a kupu pu ke kakalaioa, a hihia iho la ia.
8 Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
A helelei iho la kekahi ma ka lepo maikai, a kupu ae la ia, a hua mai la ia pahaueri ka hua. A pau kana hai ana ia mau mea, kahea mai la ia, O ka mea pepeiao lohe, e hoolohe ia.
9 Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
Ninau aku la kana mau haumana ia ia, Heaha la ke ano o keia olelonane?
10 Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
I mai la oia, Ua haawiia no ia oukou e ike i na mea pohihihi o ke aupuni o ke Akua; a i kekahi poe hoi ma na olelonane, i nana lakou, aole nae e ike, a i lohe hoi, aole nae e hoomaopopo.
11 “Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
Eia hoi ua olelonane nei. O ka hua, oia ka olelo a ke Akua.
12 Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
A o na mea ma kapa alanui, oia no ka poe i lohe; alaila hele mai ka diabolo, kaili ae ia i ka olelo mai loko ae o ko lakou mau naau, o manaoio lakou a e hoolaia.
13 Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
A o ka poe maluna o ka pohaku, a lohe lakou, apo lakou i ka olelo me ka olioli; aole hoi o lakou mole, manaoio no lakou i kekahi manawa, a i ka wa e hoaoia'i, haalele no lakou.
14 Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
A o ka mea i helelei mawaena o ke kakalaioa, oia ka poe i lohe, a hele lakou, a hihia i na manao, a me ka waiwai, a me na lealea o neia ola ana, aole hoi lakou i hoohua mai i ka hua a oo.
15 Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
Aka, o ka mea ma ka lepo maikai, oia ka poe i hoolohe, a malama hoi i ka olelo maloko a ka naau maikai a me ka hoopono, a hoohua mai i ka hua me ke ahonui.
16 “Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
Aole mea i hoa i ke kukui a huna iho malalo iho o ke poi, aole hoi e hahao malalo ae o kahi moe; aka, kauia no ia ma ka mea kaukukui, i ikeia'i ka malamalama e ka poe i komo iloko.
17 Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
No ka mea, aole mea nalo e koe i ka hoikeia, aole mea huna e pau ole i ka ikeia, a i ka puka iwaho.
18 Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Nolaila hoi e noonoo i ko oukou hoolohe ana; no ka mea, o ka mea ua loaa, e haawi hou ia'ku no ia ia; aka, o ka mea loaa ole, e kailiia'ku hoi ka mea me he mea nona la, mai ona aku.
19 Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
Alaila hele aku la ia ia kona makuwahine a me kona mau hoahanau, aole nae i hiki io na la, no ka ahakanaka.
20 Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
Hai aku la kekahi poe ia ia, i aku la, O kou makuwahine a me kou mau hoahanau, ke ku mai la mawaho, e ake lakou e ike ia oe.
21 Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
Olelo mai la oia, i mai la ia lakou, O ka poe i lohe a i malama hoi i ka olelo a ke Akua, o lakou ko'u makuwahine, a me ko'u mau hoahanau.
22 Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
Eia kekahi, i kekahi la, ee ae la ia me kana mau haumana, ma ka moku; a i mai la oia ia lakou, E holo kakou ma kela kapa o ka moanawai. A holo aku la lakou.
23 Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
A i ko lakou holo ana'ku, hiamoe iho la ia; a nou mai ka makani me ka ino maluna o ka moanawai, a piha ae la lakou i ka wai, aneane e make.
24 Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
Kii iho la lakou e hoala ia ia, i aku la, E ke Kumu, E ke Kumu, ua make makou. Alaila ala ae la ia, a papa aku la i ka makani a me ke kupikipikio o ka wai; a oki ae la ia mau mea, a malie iho la.
25 Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
I mai la oia ia lakou, Auhea la hoi ko oukou manaoio? Weliweli iho la lakou a mahalo iho la; olelo lakou ia lakou iho, Owai la hoi keia! ua olelo aku no ia i ka makani a me ka wai, a hoolohe mai no ia mau mea ia ia.
26 Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
A hiki aku la lakou i ka aina o ko Gadara e ku pono ana i Galilaia.
27 Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
Hele aku la ia mauka, halawai mai la me ia kekahi kanaka o ke kulanakauhale, ua loihi loa kona uluhia ana e na daimonio, aole ia i komo kapa, aole hoi ia i noho ma ka hale maoli, aka, ma na halekupapau.
28 Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
A i kona ike ana ia Iesu, walaau ae la ia, moe iho la imua ona, kahea ae la me ka leo nui, Heaha kau ia'u, e Iesu ke Keiki a ke Akua kiekie loa? ke noi aku nei au ia oe, mai hana eha mai ia'u.
29 Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
No ka mea, ua hookina no ia i ka uhane ino e puka mai iwaho o ua kanaka la: no ka mea, ua loohia pinepine ia e ia; a i kona paa ana i ke kaulahao a me ke kupeeia, ua moku ia ia ua mau mea paa la, a ua hookukeia'ku ia e ka daimonio i ka waonahele.
30 Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
Alaila ninau aku la o Iesu ia ia, i aku la, Owai kou inoa? Hai mai la oia, O Legeona; no ka mea, he nui no na daimonio i komo iloko ona.
31 Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
Nonoi mai la lakou ia ia i hookina ole oia ia lakou e hele i ka hohonu. (Abyssos g12)
32 A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
A he nui no ka poe puaa ilaila, e ai ana ma ka mauna; a nonoi mai la lakou ia ia e ae aku ia lakou e komo ae iloko o ua poe puaa la. Ae aku la oia ia lakou.
33 Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
A hele aku la na daimonio iwaho o ua kanaka la, a komo aku la iloko o ka poe puaa; a holo kiki iho la ka poe puaa ma kahi pali, ilalo i ka moanawai, a umiia ka hanu.
34 Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
A ike aku la ka poe kahu ia mea, naholo aku la lakou, a hoikeike aku la maloko o ke kulanakauhale a me na kauhale.
35 Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
A haele ae la na kanaka iwaho e ike ia mea; a hiki aku la io Iesu la, ike iho la i ua kanaka la noloko mai ona i puka mai ai na daimonio, e noho ana ma na wawae o Iesu, ua aahuia, a ua pono kona manao; weliweli iho la lakou.
36 Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
A o ka poe i ike maka, hai mai la ia lakou i ka mea i ola'i ua kanaka daimonio la.
37 Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
A pau hoi ko Gadara a puni i ke noi aku ia ia e hele aku mai o lakou aku; no ka mea, ua loohia lakou e ka weliweli. Ee hou iho la ia i ka moku a hoi mai la.
38 Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
A o ke kanaka mailoko mai ona i puka mai ai na daimonio, ua noi aku ia ia e noho pu ia me ia. Aka, hoihoi mai la Iesu ia ia, i mai la,
39 “Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
E hoi aku oe i kou hale, a e hoike aku i na mea nui a ke Akua i hana mai ai nou. Alaila hele ia a hoike ma ia kulanakauhale a pau, i na mea nui a Iesu i hana mai ai nona.
40 Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
Eia kekahi, i ka hoi ana mai o Iesu, halawai aloha ka ahakanaka me ia; no ka mea, e kali ana lakou a pau ia ia.
41 Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
Aia hoi, hele mai la kekahi kanaka, o Iairo kona inoa, he luna hoi ia no ka halehalawai; moe iho la ia ma na wawae o Iesu, nonoi aku la ia ia e hele mai iloko o kona hale:
42 domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
No ka mea, he kaikamahine kamakahi kana, he umikumamalua paha kona mau makahiki, a e make ana ia. A i ko Iesu hele ana, hooke ae la ka ahakanaka ia ia.
43 A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
A he wahine hoi, he umikumamalua makahiki o kona heekoko ana, ua pau kona waiwai i na kahuna lapaau, aohe o lakou mea e ola'i ia;
44 Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
Hele mai la ia mahope ona, hoopa iho la i ke kihi o kona aahu; paa koke iho la kona heekoko.
45 Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
Ninau mai la o Iesu, Nawai la wau i hoopa mai nei? A pau lakou i ka hoole, i aku la o Petero a me ka poe me ia, E ke kumu, ua hooke aku ka ahakanaka ia oe, a ua pilikia oe, a ke ninau nei oe, Nawai la wau i hoopa mai nei?
46 Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
A olelo mai la o Iesu, Ua hoopa mai no kekahi ia'u; no ka mea, ua ike au i ka puka ana'ku o ka mana mailoko aku o'u.
47 Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
A ike iho la ua wahine la, aole ia i nalo, hele haalulu ae la ia, moe iho la imua ona, hoike ae la ia ia imua o na kanaka a pau i kana mea i hoopa ai ia ia, a me kona ola koke ana iho.
48 Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
I mai la Iesu ia ia, E olioli oe, e ke kaikamahine; ua ola oe i kou manaoio; e hele hoi oe roe ka pomaikai.
49 Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
Ia ia e olelo ana, hiki mai la kekahi mai ka hale mai o ua luna halehalawai la, i mai la ia ia, Ua make kau kaikamahine; mai hooluhi oe i ke Kumu.
50 Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
A lohe ae la o Iesu, olelo mai la oia ia ia, i mai la, Mai makau oe; e manaoio wale no, a e hoolaia no ia.
51 Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
A hiki aku la oia i ka hale, aole mea e ae ana i ae mai ai e komo iloko, o Petero, a me Iakobo, a me Ioane, a me ka makuakane a me ka makuwahine wale no o ua kaikamahine la.
52 Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
Auwe iho la lakou a pau me ke kanikau ia ia. I mai la Iesu, Mai uwe oukou; aole ia i make, aka, e hiamoe ana no ia.
53 Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
A hoomauakala aku la lakou ia ia, no ka mea, ua ike io lakou ua make ia.
54 Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
A hoihoi oia ia lakou a pau iwaho, lalau iho la ia i kona lima, kahea iho la, i iho la, E ke kaikamahine, e ala!
55 Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
A hoi mai la kona uhane, a ala koke mai la oia iluna; olelo iho la oia e haawi i ai nana.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.
A pihoihoi iho la na makua ona. Papa mai la oia ia laua, aole e hai aku i keia hana ia hai.

< Luka 8 >