< Luka 8 >

1 Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
И скоро след това Исус ходеше по градове и села да проповядва и да благовестява Божието царство; и с Него бяха дванадесетте ученика,
2 da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
и някои жени, които бяха изцелени от зли духове и болести: Мария, наречена Магдалина, от която бяха излезли седем бяса,
3 Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
и Иоана жената на Иродовия настойник Хуза и Сусана и много други, които им услужваха с имота си.
4 Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
И понеже се събра голямо множество, и дохождаха при Него от всеки град, рече с притча:
5 “Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
Сеячът излезе да сее семето си; и когато сееше, едно падна край пътя; и затъпка се, и небесните птици го изкълваха.
6 Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
А друго падна на канарата; и щом поникна изсъхна, защото нямаше влага.
7 Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
Друго пък падна всред тръните; и заедно с него порастнаха тръните и го заглушиха.
8 Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
А друго падна на добра земя и като порастна, даде стократен плод. Като каза това, извика: Който има уши да слуша, нека слуша.
9 Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
А учениците Му Го попитаха за значението на тая притча.
10 Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
Той каза: На вас е дадено да знаете тайните на Божието царство; а на другите се проповядва с притчи, тъй щото, като гледат, да не виждат, и като слушат, да не разбират.
11 “Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
Прочее, ето значението на притчата: Семето е Божието слово.
12 Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
А посяното край пътя са тия, които са слушали; тогава дохожда дяволът и отнема словото от сърцата им, да не би да повярват и се спасят.
13 Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
Падналото на канарата са тия, които, когато чуят, приемат словото с радост; но те, като нямат корен, временно вярват, а когато настане изпитание, отстъпват.
14 Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
Падналото всред тръните са ония, които са слушали, и, като си отиват, заглъхват от грижи и богатства и житейски удоволствия и не дават узрял плод.
15 Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
А посятото на добра земя са тия, които, като чуят словото, държат го в искрено и добро сърце, и дават плод с търпение.
16 “Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
И никой, като запали светило, не го покрива със съд, нито го туря под легло, но го туря на светилник, за да видят светлината тия, които влизат.
17 Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
Защото няма нещо тайно, което не ще стане явно, нито потаено, което не ще се узнае и не ще излезе наяве.
18 Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Затова, внимавайте как слушате; защото който има, нему ще се даде; а който няма, от него ще се отнеме и това, което мисли че има.
19 Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
И дойдоха при Него майка Му и братята Му, но поради множеството не можаха да се приближат до Него.
20 Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
И известиха Му: Майка Ти и братята Ти стоят вън и искат да Те видят.
21 Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
А Той в отговор им рече: Майка Моя и братя Мои са тия, които слушат Божието слово и го изпълняват.
22 Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
А в един от тия дни Той влезе в ладия с учениците Си, и рече им: Да минем на отвъдната страна на езерото. И отплуваха.
23 Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
А като плуваха, Той заспа; и ветрена буря се устреми върху езерото, и вълните ги заплашваха така щото бяха в опасност.
24 Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
И дойдоха, разбудиха Го и казаха: Наставниче! Наставниче! Загиваме! А Той се събуди и смъмра вятъра и развълнуваната вода; и успокоиха се, и настана тишина.
25 Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
И рече им: Где е вярата ви? А те уплашени се чудеха, и казваха си един на друг: Кой ли ще е Тоя, който заповядва и на ветровете и на водата, и те Му се покоряват?
26 Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
И пристигнаха в Герасинската страна, която е срещу Галилея.
27 Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
И като излезе на сушата, срещна Го от града някой си човек, който имаше бесове, и за дълго време не беше обличал дреха, и в къщи не живееше, но в гробищата.
28 Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
Той, като видя Исуса, извика, падна пред Него, и рече със силен глас: Какво имаш Ти с мене Исусе, Сине на Всевишния Бог? Моля Ти се недей ме мъчи!
29 Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
Защото Исус беше заповядал на нечистия дух да излезе от човека. Понеже много пъти бе го прихващал; и връзваха го с вериги и окови и го пазеха; но той разкъсваше връзките, и бесът го гонеше по пустините.
30 Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
Исус го попита: Как ти е името? А той каза: Легион, защото много бесове бяха влезли в него.
31 Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
И молеха Го да не им заповяда да отидат в бездната. (Abyssos g12)
32 A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
А там имаше голямо стадо свини, което пасеше по хълма, и бесовете Го помолиха да им позволи да влязат в тях. И позволи им.
33 Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
И като излязоха бесовете из човека и влязоха в свините, стадото се спусна по стръмнината в езерото и се издави.
34 Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
А свинарите, като видяха станалото, прибягнаха и известиха за това в града и в селата.
35 Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
И като излязоха да видят станалото и дойдоха при Исуса, намериха човека, от когото бяха излезли бесовете, седнал при Исусовите нозе, облечен и смислен; и изплашиха се.
36 Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
И тия, които бяха видели това, разказаха им как излекувал бесния.
37 Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
И цялото множество от Герасинската околност Му се помоли да си отиде от тях, защото бяха обзети от голям страх; и Той влезе в ладията и се завърна.
38 Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
А човекът, от когото бяха излезли бесовете, молеше Му се да бъде с него; но Исус го изпрати като каза:
39 “Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
Върни се у дома си и разкажи, какви неща ти стори Бог. И той отиде и разгласи по целия град, какви неща му стори Исус.
40 Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
А когато се върна Исус, народът Го посрещна радостно, защото всички Го чакаха.
41 Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
И, ето, дойде един човек на име Яир, който беше началник на синагогата, и падна пред Исусовите нозе и Му се молеше да влезе в къщата му;
42 domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
защото имаше едничка дъщеря, на около дванадесет години, и тя беше на умиране. И когато отиваше, народът Го притискаше.
43 A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
И една жена, която имаше кръвотечение от дванадесет години, и бе иждивила за лекари целия си имот, без да може да се излекува от никого,
44 Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
се приближи изотзад та се допря до полата на дрехата Му; и на часа престана кръвотечението -.
45 Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
И рече Исус: Кой се допря до Мене? И когато всички се отричаха, Петър и ония, които бяха с Него, казаха: Наставниче, народът Те притиска и гнети, [а Ти казваш: Кой се допря до Мене?]
46 Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
Но Исус каза: Някой се допря до Мене; защото Аз усетих, че сила излезе от Мене.
47 Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
И жената, като видя, че не се укри, дойде разтреперана и падна пред Него и извика пред всичките люде, по коя причина се допря до Него, и как на часа оздравя.
48 Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
А той - рече: Дъщерьо, твоята вяра те изцели; иди си с мир!
49 Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
Докато Той още говореше, дохожда някой си от къщата на началника на синагогата и казва: Дъщеря ти умря; не затруднявай Учителя.
50 Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
А Исус като дочу това, отговори му: Не бой се; само вярвай, и тя ще се избави.
51 Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
И когато дойде в къщата, не остави никой да влезе с Него, освен Петра, Иоана, Якова и бащата и майката на момичето.
52 Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
И всички плачеха и го оплакваха. А Той им рече: Не плачете; защото не е умряло, а спи.
53 Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
А те Му се присмиваха, понеже знаеха, че е умряло.
54 Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
Но Той го хвана за ръката, и извика: Момиче, стани!
55 Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
И върна се духът му, и то на часа стана; и Той заповяда да му дадат нещо да яде.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.
И родителите му се учудиха; а Той им заръча да не казват никому за станалото.

< Luka 8 >