< Luka 7 >

1 Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
Як же скінчив усї глаголи свої в слух людям, увійшов у Капернаум.
2 A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
В одного ж сотника слуга недугуючи мав умирати, котрий був йому дорогий
3 Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
Почувши ж про Ісуса, післав до Него старших Жидівських, благаючи Його, щоб, прийшовши, спас слугу його.
4 Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
Вони ж, прийшовши до Ісуса, благали Його пильно, говорячи: Що достоєн він, щоб йому зробив се:
5 gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
любить бо нарід наш, і шкоду він збудував нам.
6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
Ісус же пійшов з ними. І як вже він недалеко був од будинка, вислав до Него сотник другів, говорячи Йому: Господи, не трудись, бо я недостоєн, щоб Ти під стелю мою ввійшов;
7 Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
тим і себе не вважав достойним до Тебе прийти; тільки промов слово, то й одужає слуга мій.
8 Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
Бо й я чоловік під властю поставлений, маючи під собою воїнів; і скажу сьому: Йди, то й іде, а другому: Прийди, то й прийде, а слузї моєму: Роби оце, то й зробить.
9 Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
Почувши ж се Ісус, дивувавсь йому, й, обернувшись до йдучого за собою народу, рече: Глаголю вам: Навіть в Ізраїлі, такої віри не знайшов я.
10 Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
І вернувшись послані у будинок, знайшли недужнього слугу здоровим.
11 Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
І сталось опісля, ійшов Він у город, званий Наш, і йшло з Ним доволї учеників Його, й багато народу.
12 Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
Як же наближився до городських воріт, аж ось винесено мертвого, сина єдиного в матері своєї, вона ж була вдова; й багато народу з городу було з нею.
13 Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
І побачивши її Господь, змилосердивсь над нею, і рече їй: Не плач.
14 Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
І приступивши, приторкнув ся до мар; ті ж, що несли, з'упинились. І рече: Молодче, тобі глаголю: встань.
15 Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
І сїв мерлець, і почав говорити. І оддав його матері його.
16 Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
Обняв же страх усїх; і прославляли вони Бога, кажучи: Що пророк великий устав між нами, й навідав Бог людей своїх.
17 Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
І розійшлось слово се по всїй Юдеї про Него й по всїй околицї.
18 Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
І сповістили Йоана ученики його про все те.
19 ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
І покликавши двох ученикїв своїх Йоан, післав до Ісуса, кажучи: Ти єси грядущий, чи иншого ждати нам?
20 Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
Прийшовши ж до Него чоловіки, казали: Йоан Хреститель прислав нас до Тебе, кажучи: Ти єси грядущий, чи иншого ждати нам?
21 A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
Того ж часу сцїляв Він многих від недуг і ран, і духів лихих, і многим слїпим давав прозрїннє.
22 Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
І озвавшись Ісус, рече їм: Ідїть сповістіть Йоана, що бачили й чули: як слїпі прозирають, криві ходять, прокаженні очищають ся, глухі чують, мертві встають, і вбогі благовіствують.
23 Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
І блажен, хто де зблазнить ся мною.
24 Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
Як же пійшли посланці Йоанові, почав глаголати до народу про Йоана: Чого виходили ви дивитись у пустиню? На тростину, що вітер колише?
25 In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
Або чого ж виходили їй дивитись? На чоловіка, в мягку одежу одягненого? Ось ті, що в одежі пишній та роскоші, панують у царських дворах.
26 Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
Або чого виходили ви дивитись: На пророка? Так, глаголю вам, і більш пророка.
27 Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
Се той, про кого написано: Ось я досилаю ангела мого перед лицем Твоїм, що приготовить дорогу Твою перед Тобою.
28 Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
Глаголю бо вам: Більшого між нарожденими від жінок пророка над Йоана Хрестителя нема; найменший же у царстві Божім більший від него.
29 (Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
І ввесь народ слухаючий, і митники, справдили Бога, хрестившись хрещеннєм Йоановим.
30 Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
Фарисеї ж та законники раду Божу про них відкинули, не хрестившись від него.
31 Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
Рече ж Господь: Кому ж оце уподоблю людей роду сього? й кому подобні вони?
32 Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
Подобні вони дітям, що сидять на торгу та гукають одно на одного, та й кажуть: Ми сурмили вам, а ви не скакали; ми голосили вам, а ви не плакали.
33 Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
Прийшов бо Йоан Хреститель, що хлїба не їсть, анї вина не пє, і кажете: Диявола мав.
34 Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
Прийшов Син чоловічий, що їсть і пє, і кажете: Ось чоловік прожора та пяниця, митникам друг і грішникам.
35 Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
І справдилась премудрість од дітей своїх усїх.
36 To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
Просив же хтось Його з Фарисеїв, щоб їв з ним. І, ввійшовши з господу Фарисееву, сїв за столом.
37 Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
І ось жінка у городі, що була грішниця, довідавшись, що сидить за столом у господї Фарисеевій, принісши любастровий збаночок мира,
38 ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
і ставши коло ніг Його ззаду, плачучи, почала обмивати ноги Його слїзми, й волоссєм голови своєї обтирати; й цілувала ноги Його, й мастила миром.
39 Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
Бачивши ж Фарисей, що запросив Його, казав сам у собі, говорячи: Коли б сей був пророк, знав би, хто й яка се жінка, що приторкуєть ся до Него; бо грішниця вона.
40 Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
І озвавшись Ісус, рече до него: Симоне, маю тобі щось сказати. Він же каже: Учителю, скажи.
41 Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
Два довжники були в одного вірителя: один завинив пятьсот денариїв, другий же пятьдесять.
42 Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
Як же не мали чим оддавати, обом простив він. Хто ж оце з них, скажи, більш його любити ме?
43 Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
Озвав ся ж Симон і Каже: Думаю, що той, кому більш простив він. Він же рече йому: Право судив єси.
44 Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
І, обернувшись до жінки, рече Симонові: Чи бачиш ти сю жінку? Увійшов я в твою господу, - води на ноги мої не дав єси; ся ж слїзми обмила ноги мої, і волоссєм голови своєї обтерла.
45 Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
Цїлування не дав єси менї; ся ж, відколи ввійшов я, не перестала цілувати ноги мої.
46 Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
Оливою голови моєї не намастив єси; ся ж миром намастила ноги мої.
47 “Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
Тим тлаголю тобі: Оставляють ся гріхи її многі, бо возлюбила много; кому ж мало оставляєть ся, мало любить.
48 Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
Рече ж їй: Оставляють ся гріхи твої.
49 Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
І почали ті, що вкупі сиділи, казати в собі: Хто сей, що й гріхи відпускає?
50 Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”
Рече ж до жінки: Віра твоя спасла тебе; йди з упокоєм.

< Luka 7 >